Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

0
116
Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

An jiyo Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja yana ba da umarnin jami’an tsaronsa da su yi wa wani malamin addinin Islama cin mutunci a yayin bikin addu’ar Fidda’u ga matar mataimakinsa, Hajiya Zainab Yakubu Garba da ta rasu.

Lamarin wanda ya auku a Minna a ranar Juma’a, ya auku ne a lokacin da malamin ya sadaukar da kansa domin gudanar da addu’a, lamarin da aka ce ya harzuƙa Gwamna Bago.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin Gwamna Bago yana jawabi ga masu jajantawa, inda ya nuna cewa za a iya gudanar da addu’o’i ga marigayiyar a cikin gida, kafin daga bisani ya fusata a lokacin da malamin ya fito.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Ya tuhumi malamin, sannan ya umurci jami’an tsaronsa da su ɗauki mataki, inda ya umarce su da su yi masa mari mai kyau sannan su kama shi.

Shaidu da suka halarci taron sun nuna kaɗuwa dangane da wannan hali na gwamnan, inda suka yi la’akari da irin tsaurin ra’ayinsa ga malamin.

Wannan lamari dai ya ƙara rura wutar zarge-zargen da ke tattare da yadda Gwamna Bago ke da alaƙa da cin zarafi ga mataimaka da magoya bayansa, kamar yadda SaharaReporters ta ruwaito kuma majiyar gwamnan ta tabbatar.

Kalli bidiyon a nan:

Leave a Reply