Gobe Asabar za a fara Azumin watan Ramadan a Najeriya – Fadar Sarkin Musulmi

0
7
Gobe Asabar za a fara Azumin watan Ramadan a Najeriya - Fadar Sarkin Musulmi

Gobe Asabar za a fara Azumin watan Ramadan a Najeriya – Fadar Sarkin Musulmi

Daga Ibraheem El-Tafseer

Fadar mai alfarma sarkin Musulmin Najeriya, ta sanar da ganin jinjirin watan Ramadan da maraicen ranar Juma’a.

Cikin wata sanarwa da Sarkin Musulmin, Alhaji Sa’ad Abubakar lll ya karanta a fadarsa, ya ce an ga watan a sassan ƙasar daban-daban.

KU KUMA KARANTA:Gwamnan Yobe ya yi ƙira ga jami’an tsaro da su tsaurara tsaro a watan Ramadan

Don haka ne ya ayyana ranar Asabar 1 ga watan Maris a matsayin 1 ga watan Ramadan 1446 (2025).

Tuni dai hukumomin Saudiyya suka sanar da ganin watan a ƙasar, inda suka ayyana gobe Asabar a matsayin ɗaya ga watan Ramadan a Saudiyya.

Leave a Reply