Falasɗinu za ta bayar da shaida a gaban Kotun Duniya

Ƙasar Palestine za ta zama ƙasa ta farko cikin ƙasashe 52 da za su yi magana a Kotun Duniya yayin da kotun za ta shafe kwana shida tana sauraren ƙarar da aka shigar a gabanta.

“Muna so mu ji sabbin kalamai daga kotun” in ji Omar Awadallah, shugaban sashen Majalisar Ɗinkin Duniya a Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasɗinu, gabannin soma sauraren ƙarar.

KU KUMA KARANTA: WHO ta taimaka wajen kwashe marasa lafiya 14 daga Asibitin Nasser da ke Gaza da aka yi wa ƙawanya

“Akwai buƙatar su yi la’akari da batun kisan kiyashi a koken Afirka ta Kudu,” kamar yadda ya bayyana inda yake bayani dangane da wani koken na daban da ke gaban kotum. “A yanzu muna so su yi la’akari da batun wariyar launin fata.”


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *