Connect with us

Labarai

ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro – Badaru

Published

on

ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro - Badaru

ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro – Badaru

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Afirka ta Yamma ECOWAS tana buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don samar da ƙaƙƙarfar rundunar tsaro da za ta yi yaƙi da ta’addanci, a cewar ɗaya daga cikin zaɓuka biyun da hukumomin tsaro na ƙasashen yankin ke duba yiwuwarsu a taron da suka yi a jiya Alhamis.

Ministocin Tsaro da na Kuɗi na Ƙasashen ECOWAS sun yi taron a Abuja, babban birnin Najeriya, inda suka tattauna kan yanke shawarar yawan dakarun da kuma yawan kuɗaɗen da ake buƙata don samar da ita.

Afirka ta Yamma na fama da matsalolin juyin mulki, lamarin da yake zama matsala ga tsarin siyasa da jawo rarrabuwar kai tsakanin ƙasashen yankin.

KU KUMA KARANTA: Masana sun yi ƙira da a yi sabbin sauye-sauye ECOWAS

A watan Janairu, shugabannin mulkin soji na Nijar da Burkina Faso da Mali sun yanke shawarar ficewa daga ƙungiyar mai mambobin ƙasashe 15.

Ministan Tsaron Najeriya ya shaida wa taron cewa akwai zaɓi biyu a samar da rundunar yankin: Daya za a kashe dala biliyan 2.6 duk shekara a kan runduna mai dakaru 5,000, dayan kuma za a kashe dala miliyan 481 a dakaru 1,500
“Waɗannan alkaluma sun nuna muhimmancin aikin da ke gabanmu,” in ji Badaru.
“Don haka ya zama wajibi mu yi nazari sosai kan zabin duba da irin kalubalen da yankinmu ke fuskanta a halin yanzu da kuma matsalolin kudi da kasashe mambobinmu ke fuskanta.”

Tun a shekarar 2020, sojoji a kasashen uku suka yi juyin mulki suna zargin shugabannin farar hula da ƙyale masu da’awar jihadi su samu galaba.

Da hawansu kan mulki, sojojin sun yi watsi da yarjejeniyoyin tsaro da aka ƙulla da sojojin Amurka da Faransa da kuma na Majalisar Dinkin Duniya tare da gayyatar Rasha da su maye gurbinsu.

Ministan Tsaron Nijeriya ya kara da cewa ba za a yi amfani da rundunar yankin wajen ɗaukar mataki a kan juyin mulkin ba, illa kawai yaƙi da ta’addanci. Ana sa ran kowace ƙasa mamba za ta ba da gudunmawar wani kaso, in ji shi.

Shugaban hukumar ECOWAS Omar Touray ya ce ba za a cire mambobin da aka dakatar daga cikin rundunar yankin ba.

“An yi imanin ba za mu iya yaki da ta’addanci mu kadai idan har wasu ba su shiga ba,” in ji Touray.

“Ko da yake ana iya dakatar da wasu kasashe amma ya kamata a bar su su shiga tarukan da suka shafi tsaro, shi ya sa muka gayyaci dukkan kasashe mambobi 15 da su halarci wannan muhimmin taro.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Published

on

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

 

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya amince da naɗin sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya guda takwas da za su cike guraben da ake da su a wasu jihohi da shiyyoyin ƙasar a ma’aikatan gwamnati.

Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da bayanai ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a jiya Juma’a, inda ya ce an naɗa sabbin sakatarorin dindindin ɗin ne bayan da ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ya gudanar da aikin zaɓo su.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Sakatarorin su ne: Dr Emanso Umobong Okop – Akwa-Ibom, Obi Emeka Vitalis – Anambra, Mahmood Fatima Sugra Tabi’a – Bauchi, Danjuma Mohammed Sanusi – Jigawa, Olusanya Olubunmi – Ondo, Dr Keshinro Maryam Ismaila – Zamfara, Akujobi Chinyere Ijeoma (Kudu-maso-Gabas)) da kuma Isokpunwu Christopher Osaruwamwen (Kudu-maso-Kudu).

“Shugaban ya yi hasashen cewa sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya za su yi aiki da ƙwazo, himma da riƙon amana ga ƙasa wajen gudanar da ayyukansu tare da tabbatar da ingantacciyar hidima ga al’ummar Najeriya,” in ji sanarwar.

Continue Reading

Labarai

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Published

on

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

 

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ba da Naira dubu hamsin-hamsin ga iyalai miliyan 3.6 har tsawon wata uku a faɗin Nijeriya.

Wannan na ɗaya daga cikin yarjejeniyoyi da aka cimma a ganawar da Tinubu ya yi da gwamnonin jihohi 36 na ƙasar nan a yau Alhamis a Abuja.

Shugaban ya ba da umarnin raba kuɗin ga iyalai dubu 100 a kowace jiha har na tsawon watanni uku.

Sauran batutuwa da aka cimma a ganawar sun haɗa da:

* Bawa iyalai 100,000 a kowace jiha tallafin N50,000 na tsahon wata uku.

* Ware Naira biliyan 155 domin siyen kayan abinci da za a tallafawa masu ƙaramin ƙarfi kan farashi mai rahusa.

* Baiwa kowace jiha Naira biliyan 10 domin sayen motocin sufuri masu aiki da iska gas domin sauko da farashin kuɗin zirga-zirga.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

* Gaggauta fara aikin hanyar da ta tashi daga Sakkwato zuwa Badagary a Lagos. Hanyar zata ratsa ƙauyuka kimanin 216, madatsun ruwa (dams) guda 58, ƙananan hukumomi 156 da manyan garuruwa 39 da kuma gonaki da suka kai kimanin hectare miliyan ɗaya. Titin zai ratsa jihohin Sokoto da Kebbi da Niger da Kwara da Oyo da Ogun da kuma Lagos.

* Shugaba Tinubu ya kuma amince da biyan kuɗin aikin hanyar jirgin ƙasa daga Fatakwal zuwa Maiduguri wadda za ta ratsa jihohin Rivers da Abia da Enugu da Benue da Nasarawa da Plateau da Bauchi da Gombe da Yobe da kuma Borno.

* Haka nan an amince da biyan kuɗin da ake buƙatar domin yin aikin hanyar jirgin ƙasa da ta taso daga Ibadan zuwa Abuja a wani ɓangare na aikin dogo da ya tashi daga Lagos zuwa Kano. Aikin zai haɗa jihohin Lagos da Ogun da Oyo da Osun da Kwara da Niger da Abuja da Kaduna da kuma Kano.

* Shugaban ƙasa ya kuma bada umarnin cigaba da aikin hanyar Lagos zuwa Calabar wadda kuma zata yi rassa a jihohin Benue da Kogi da Abuja da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Published

on

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin jihar Kano ta yi watsi da batun ɗaga tutar masarauta da aka yi a gidan sarki na Nassarawa wurin da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ke zaune, inda ta bayyana hakan da ƙoƙarin jan hankalin jama’a kawai.

Tutar, wata alama ce ta iko dake nuni da cewar Sarki na nan, a kullum ana ɗaga ta da misalin ƙarfe 6 na safe a kuma sauƙe ta da misalin ƙarfe 6 na yamma. Duk lokacin da sarki ba ya cikin fada ko ya yi balaguro za ta kasance a sauƙe.

Da safiyar ranar Alhamis, aka lura cewar an ɗaga tutar da misalin ƙarfe 6 na safiya a fadar Nassarawa, abin da ya haifar da kace-nace dama raɗe-raɗi.

Kowane daga cikin Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II na iƙirarin shi ne Sarkin Kano kuma suna ci gaba da aiwatar da ayyukan sarauta.

KU KUMA KARANTA:An sauya Kwamishinan ’yan sandan Kano

Gwamnatin jihar ce ta sauƙe Aminu Ado Bayero tare da sake naɗa Muhammadu Sanusi biyo bayan yiwa dokar masarautu ta Kano kwaskwarima.

An ɗaga irin wannan tuta a fadar gidan Rumfa, inda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ke zaune.

Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya yi fatali da batun ɗaga tuta a fadar Nassarawar, inda yace hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma.

Ya shaidawa manema labarai cewar, “hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma. Amma babu shakku ko tantamar cewar Sanusi ne Sarkin Kano.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like