Direban da ya kashe masu shara a Legas, ya miƙa kansa ga ’yan sanda

Wani direba da ake zargi da take ma’aikatan shara har lahira a lokacin da suke tsaka da aiki a Legas ya miƙa kansa ga hukuma.

Ana zargin zargin direban ya yi ajalin masu sharan ne bayan da ya taho a guje inda ya kaɗe su a lokacin da suke tsaka da aikinsu a gefen babban titin Gbagada a ranar Litinin.

Kakakin ’yan sanda a jihar, Benjamin Huneyin, ya tabbatar cewa direban da ya miƙa kansa ga rundunar yana nan a hannunsu.

Amma jami’in ya ce “ abun da ya faru ba kisa ba ne haɗari ne, kuma za mu gurfanar da shi gaban kotu bisa zargin kisan kai, amma ba na ganganci ba”.

KU KUMA KARANTA: Ya kashe direba don ya ajiye mota a inda aka hana – ‘Yan sanda

A baya dai an ruwaito cewa, direban ya kaɗe ma’aikatan sharar su biyu, suka mutu nan take, shi kuma ya tsere ya bar motar sa a wajen da abin ya faru.

Ana zargin hakan ta faru ne a bayan ya taho a guje da nufin tsere wa jami’an kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar, waɗanda suka biyo shi a baya.

Sai dai ma’aikatar sufiri ta jihar ta ce babu wani jami’in ta da ke da hannu a faruwar al’amarin, ‘amma bayan binciken ’yan sanda, idan akwai ma’aikacinmu da ke da hannu za mu hukunta shi daidai da yadda doka ta ce.’


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *