Dalilin da ya sa mu ka sake ƙara farashin man fetur — NNPC

0
80
Dalilin da ya sa mu ka sake ƙara farashin man fetur — NNPC

Dalilin da ya sa mu ka sake ƙara farashin man fetur — NNPC

Kamfanin man fetur na ƙasa (NNPCL) ya kare matakin da ya ɗauka na ƙara kuɗin man fetur a karo na biyu cikin wata guda.

Lawal Sade, shugaban NNPCL sashen kasuwanci da cinikayya na kamfanin ya ce hakan ta faru ne saboda yanayin farashin ɗanyen mai a kasuwannin duniya da kuma yanayin canjin kuɗin waje.

KU KUMA KARANTA:Ba mu muka ƙara farashin man fetur ba — Gwamnatin Tarayya

Sai dai ya ce NNPCL na wa ‘yan Najeriya albishir cewa farashin zai iya saukowa idan sauran matatun mai na cikin gida suka fara aiki gadan-gadan.

BBC Hausa ta rawaito cewa Sade ya kuma nemi afuwar ‘yan Najeriya game da matakin ƙarin.

Leave a Reply