Connect with us

Labarai

Bana za a samu ambaliyar ruwa a jihar Ekiti – NEMA

Published

on

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa, (NEMA), ta shawarci mazauna jihar Ekiti da su ɗauki matakan kariya domin kaucewa ambaliyar ruwa da aka yi hasashen zai auku a jihar nan gaba a wannan shekara.

Shugaban ayyuka na NEMA a jihohin Ekiti da Ondo, Ƙadiri Olanrewaju ne ya yi wannan gargaɗin yayin wani taron wayar da kan jama’a da aka gudanar a kasuwannin Oja-Bisi, Oja-Oba da Fayose ranar Laraba a Ado-Ekiti.

Mista Olanrewaju ya ce hasashen da hukumomin da abin ya shafa ya sanya jihar Ekiti cikin jihohin da ake sa ran za su fuskanci ambaliyar ruwa sakamakon ƙaruwar ruwan sama.

KU KUMA KARANTA: Za a samu ambaliyar ruwa a jihar Kwara – NEMA

Ya ce galibin ƙananan hukumomin jihar na fama da ambaliyar ruwa tare da yin kasada sosai sakamakon ruwan sama da aka yi a lokaci guda.

Shugaban hukumar ta NEMA ya ƙara da cewa wayar da kan ‘yan kasuwar kan haɗarin ambaliya da yaruka daban-daban kamar Ingilishi da Pidgin da Igbo da Hausa da kuma yaren Ekiti shi ne maƙasudin gudanar da taron.

Ya ce, “Kowannenmu ya shaida yadda ambaliyar ruwa ta auku a Najeriya a baya-bayan nan, wadda ta yi sanadin salwantar rayuka, da raba dubban mutane, tare da lalata dukiyoyi na miliyoyin naira.

“Ambaliya tana haifar da ɓarkewar muhalli. “Saboda haka, ya zama dole ga al’umma, ɗaiɗaikun mutane da hukumomi su ɗauki matakan da suka dace.

“Muna buƙatar mu yi imani cewa rigakafin ya fi kyau kuma mai rahusa fiye da magani, tare da la’akari da batutuwan sauyin yanayi da mahimmanci.”

Mista Olanrewaju ya buƙaci ‘yan Najeriya da su yi biyayya ga gargaɗin da ma’aikatar yanayi ta yi kan ambaliyar da ke tafe, yana mai cewa hakan zai taimaka matuƙa wajen rage illar ambaliyar.

Hakazalika, Babban Manaja na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Ekiti, Jide Borode, ya shawarci ‘yan kasuwa da su guji ɗabi’ar zubar da shara a magudanun ruwa.

Har ila yau, Daraktan hukumar kashe gobara ta jihar Ekiti, Andrew Famosaya, ya buƙaci mazauna Ekiti da su daina sare bishiyoyi ba bisa ka’ida ba.

Ya ce a maimakon haka ya kamata mazauna yankin su riƙi noma da dashen itatuwa don hana sare dazuzzuka, wanda zai iya haifar da ambaliya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like