Connect with us

Labarai

Ban janye takarata ba, inji ɗan takarar gwamnan jami’yyar NNPP a Ogun

Published

on

Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP a jihar Ogun, Olufemi Oguntoyinbo, a ranar Asabar, ya yi kira ga al’ummar jihar da su yi watsi da bayanan ƙarya da ake yaɗawa cewa ya fice daga jam’iyyar siyasa a jihar.

Oguntoyinbo, a wata sanarwa da ya sanyawa hannu da kan sa, ya ce har yanzu yana nan kan fafutukar ‘yantar da al’ummar jihar daga hannun injinan siyasa, waɗanda jarin kasuwancinsu, farfaganda ce ta siyasa.

Ya bayyana wannan jita-jita da cewa ba gaskiya ba ne, kuma zagon ƙasa ne da jam’iyyun adawa ke yi don ɓata sunan sa da ke ƙara haɓɓaka.

“Jam’iyyar NNPP ta kasance jam’iyya daya tilo da ke da muradin talakawa, matasa da kuma jam’iyyar da za ta ba matasa ilimi kyauta da kuma samar da guraben aikin yi ga kowa da kowa.

KU KUMA KARANTA: EFCC ta Kama Ɗan takarar Jam’iyyar NNPP a Kogi

“Jita-jitar cewa na fice daga takarar gwamna a jihar Ogun ba gaskiya ba ne, kuma baƙar magana ce kawai. Jam’iyyar NNPP har yanzu tana cikin tseren.

“Bayan da na zagaya dukkan ƙananan hukumomi 20 da ke jihar, matakin karɓuwar da na samu daga masu zaɓe ya sanya sauran jam’iyyun siyasa tada zaune tsaye, don haka, buƙatar ‘yan siyasa su zaɓi farfagandar siyasa, ƙarya, yaɗa bayanan ƙarya da yaudara.”

Oguntoyinbo ya ci gaba da cewa al’ummar jihar sun riga sun san halin da wasu ‘yan siyasa ke yi wanda ba za su iya kai su ko’ina ba a zaɓen gwamna.

Ɗan takarar gwamnan na NNPP ya ce, “Ina so in yi amfani da wannan hanyar domin in yaba wa waɗanda suka yi imani da iyawa da ƙarfina wajen ciyar da jihar gaba.

“Ina so in tabbatar wa mutanen jihar Ogun cewa ba ni cikin wata tattaunawa da wata jam’iyya ko ɗan takara, har yanzu ina cikin takara kuma nasara tamu ce,” in ji shi.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Ana barazana ga rayuwata, ɗan takarar gwamnan a Legas ya koka | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like