No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban ƙungiyar malaman Jami’o’i ta Najeriya, Farfesa Emmanuel Osodoke, ya ce mambobin ƙungiyar za su fuskanci wahala wajen komawa jami’o’insu a ranar Litinin saboda basu da kuɗin mota.

Shugaban na ASUU ya bayyana haka ne a jiya Lahadi, yayin tattaunawa da gidan talabijin na Channels dangane da janye yajin aikin na ASUU a cikin wani shiri mai suna Sunday Politics.

Farfesa Osodoke ya ce a lokutan baya malaman Jami’a na zama a gidajen da aka tanada musu kusa da makaranta, amma a yanzu ba haka lamarin yake ba domin suna zaune ne nesa da Jami’oin da suke koyarwa saboda yawancinsu basa samar musu wuraren zama.

“A can baya, malami zai iya taka wa da kafa yaje makaranta saboda suna zaune a cikin gidaje da aka tanada musu, amma a yanzu lamarin ya sauya, inda suke tafiyan kilomitoci 20 zuwa 30 kafin isa makaranta. Ta ya ya za su iya biyan kuɗin mota zuwa aiki,” in ji Osodoke.

Ya ce za su fuskanci wahalhalu wajen biyan kuɗin motar komawa aiki domin koyar da ɗalibai saboda ba a biya su ba har na tsawon wata takwas.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...