Connect with us

Labarai

Anya Facebook dandalin sada zumunta ne kuwa? (I)

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer
(eltafseerpen@gmail.com)

Kafar sadarwa ta Facebook, ɗaya ne daga cikin kafofin sadarwa na zamani wanda ake yaɗa saƙonni a soshiyal midiya cikin gaggawa. Facebook, ɗaya ne daga cikin ‘applications’ (manhajoji) dangogin su Twitter, Instagram, Telegram, Snapchat da sauransu. Kamar a Nijeriya kam, Facebook ya fi shahara a yanzu, tun da an rufe kafar sadarwa ta Twitter. Ana yiwa Facebook laƙabi da kafar sada zumunta.

Tun da a Facebook ana iya haɗuwa da mutanen da ba a sansu ba, kuma a ƙulla alaƙa mai ƙarfi, har ta kai an ziyarci juna, daga nisan garuruwa. Facebook yana haɗa zumunci sosai, sannan yana raba zumunci sosan gaske.

Nasan ba sabon abu bane, haɗuwa ta dalilin Facebook har a ziyarci juna daga nisan jihohi a faɗin Nijeriya. Wannan ya sha faruwa, akwai dalilai da yawa kan haka.

KU KUMA KARANTA: Yadda ake tantance (Verifying) Facebook account da Facebook Page

Kuma zumunci ya ƙullu yadda har idan wani abin farin ciki ko na baƙin ciki ya faru da ɗaya, sukan ziyarci juna. Facebook yana haɗa zumunci tsakanin namiji da mace har ya kai ga sun yi aure. Ni ma akwai abokina da dalilin Facebook suka haɗu da matar da ya aura, kuma har yanzu suna tare. Facebook yana haɗa abubuwa da yawa har da baɗala.

Akwai group-group ɗin na sada zumunta da yawa a Facebook, wanda ya haɗa mutane da dama, maza da mata, ana kuma sadar da zumunta ɗin.

Misalin ɗaya daga cikin irin waɗannan group ɗin shi ne group ɗin ‘Home Of Solace’ wanda ko a shekaru biyu baya sun shirya taro, kuma da yawa daga cikin ‘yan group ɗin sun halarta, an ci, an sha, an yi raha, sannan aka ɗauki hotuna. Zumunci ya ƙullu tsakanin da dama daga cikinsu.

Facebook wani wuri ne da mutane suke rubuta ra’ayoyinsu da nufin isar da saƙo, cikin harsunan da suke buƙata saƙon ya isa. Kamar mu a nan Nijeriya, an fi yin rubutun da yarukan Hausa, Turanci, Larabci da Faransanci. Da farko idan mutum ya buɗe shafin Facebook, akwai buƙatar yasan da wane dalili ya buɗe shafin Facebook ɗin.

Idan saƙo yake so yana isarwa, to sai ya duba ya ga da wane yare ya kamata ya yi rubutu wajen isar da saƙon, domin saƙon ya isa ga wanda aka yi dominsu. Wasu suna hawa Facebook ne don su karanta labarai da sauransu. Wasu kuma suna hawa Facebook ne don su ci mutuncin wasu.

Akwai Gidauniyoyi (Foundations) na neman taimako da yawa da suke sako hotunan waɗanda ake nema wa taimakon a shafukansu na Facebook. Kuma tabbas ana samun taimakon sosai a Facebook ɗin. Akwai misalai da yawa kan haka. Hajiya Fauziyya D. Sulaiman ɗaya ce daga cikinsu.

Facebook ya kasance wajen samun labarai cikin gaggawa. Kusan dukkan kafafen yaɗa labarai na jaridu da gidajen Talabijin da Rediyo duk suna da shafi a Facebook wanda suke wallafa labaransu a ciki. Da zarar labari da ɗumi-ɗumi ya samu, za ka ga suna ta rige-rige wajen wallafa wa a shafukansu.

Hakan yasa mafi yawan labarai a Facebook ake fara gani, kafin a samu cikakken labarin daga baya. Facebook ɗin kuma ya shahara wajen kawo labarai na ƙanzon kurege, shi ya sa da yawan mutane ba sa yarda da labaran Facebook, har sai sun ga wata jarida ta gaske ta wallafa labarin a shafinta.

Abin da ya sa nace jarida ta gaske shi ne, jaridun bogi suna nan birjik a Facebook. Da zarar mutum ya sayi babbar waya, to shi ma ya zama ɗan jarida. Abin da yake ta faruwa kenan yanzu a Facebook da WhatsApp.

Wasu kuwa suna hawa Facebook ne don ganin labaran ban dariya (comedy), don nishaɗi da rage damuwa. Wasu kuma fasadi kawai suke yaɗa wa a Facebook. Ko kunya babu za ka ga suna ta furta kalaman batsa da rashin tarbiyya iri-iri a bidiyo su ɗora a Facebook da sunan tallan magani ko kuma yaɗa iskanci.

Haka kuma Facebook ya zama wajen hada-hadar kasuwanci iri-iri. Kusan dukkan masu manyan masana’antu, da masu manyan shaguna har da masu matsakaitan kasuwanci, duk suna da shafuka da suke tallata harkokin kasuwancinsu ta hanyoyin rubuce-rubuce a Facebook, haɗe da hotuna da Bidiyon yadda kasuwancin nasu yake.

Za mu ci gaba…

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Yadda za ka kare shafinka na Facebook da Twitter daga masu ƙwace | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like