Connect with us

Kudanci

An gano gawarwarkin ma’auratan aka sace watanni biyu bayan an biya N7.5 kuɗin fansarsu

Published

on

An yi jana’izar wasu ma’aurata da masu garkuwa da su suka kashesu, duk da biyan kuɗin fansa.

Mutumin, Mista Emmanuel Chukwuemeka, mai shekaru 36, da matarsa, Mrs Chinwendu Chukwuemeka, mai shekaru 30, wasu da ba a tantance ba ne suka yi garkuwa da su tare da kashe su. An binne su ne a garinsu da ke Isiekwulu, Ukpo, a ƙaramar hukumar Dunukofia ta jihar Anambra a ranar alhamis. Jana’izar nasu ya jefa al’ummar yankin cikin makoki.

An ce ma’auratan suna komawa gidansu ne, bayan sun halarci wani shiri a Holy Ghost Adoration da ke Uke, a ƙaramar hukumar Idemili ta arewa, lokacin da aka yi garkuwa da su.

KU KUMA KARANTA:Masu garkuwa da mutane sun kashe wani ɗan kasuwa bayan karɓar kuɗin fansa

Rahotanni sun nuna cewa ma’auratan na tare da jaririnsu ɗan wata huɗu, wanda masu garkuwa da mutane suka bar shida a cikin mota, yayin da suka tafi da iyayensa.

Wata majiya ta ce da farko ‘yan uwansu sun biya masu garkuwa da mutanen kuɗi naira miliyan 5, amma sai masu garkuwar suka buƙaci a ƙara musu naira miliyan biyu da rabi lamarin da ya ɗauki lokaci a kafin a tara, saboda sai da suka sayar da wani ɓangare na filayensu domin tattara kuɗin.

Masu garkuwa da mutanen, bayan sun karɓi kuɗin fansar da suka buƙata sun kashe wayoyinsu. Bayan kimanin watanni biyu, al’ummar garin sun ga gawarwakin ma’auratan a kan hanyar Uke zuwa Nnobi, inda aka ɗaure gawarwakin da sarƙoƙi.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Yadda mace ta tono gawar tsohon mijinta, tayi faɗa da ɗanta kan dukiyar gado | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hatsari

Jirgin sama mai sauƙar ungulu ya faɗo a Legas

Published

on

Wani jirgin sama mai sauƙar ungulu ya yi hatsari a yankin Ikeja da ke Jihar Legas a kudancin Najeriya.

Wani jami’in hukumar ba da agajin gaggawa ta Legas ya ce jirgin ya kama da wuta jim kaɗan bayan rikitowarsa da tsakar ranar Talata a kusa da filin jirgin sama na Murtala Muhammad.

KALLI CIKAKKEN BIDIYON ANAN:

Hukumar agajin gaggawa ta Najeriya, ‘National Emergency Management Agency’ (NEMA), ta ce mutum huɗu ne ke cikin jirgin kuma an ceto su da ransu.
Jami’in NEMA mai kula da sashen kudu maso yamma, Ibrahim Farinloye, ya ce ba su kai ga gano mamallakin jirgin ba ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Lamarin ya faru ne shekara uku bayan wani jirgin Helikwafta mallakar kamfanin Quorom Aviation ya faɗo a yankin Opebi na Legas ɗin a watan Agustan 2020.

Continue Reading

'Yansanda

Da wane dalili ‘yan sanda suka lakaɗa wa ɗan Okada duka a Legas?

Published

on

Wani ɗan Okada, mai suna Alasan Usman matashi mai ƙoƙarin neman na kansa domin rufawa kansa da ‘yan uwansa asiri.

A ranar jumu’a ‘yan sanda a jihar Legas suka tare shi suka ce ya kawo babur ɗinsa duk da dai bai san laifin da ya aikata ba, sai ya ƙi ya basu. Saboda ya ƙi basu suka masa duka sai kace ɓarawo sai da suka yi masa jina-jina yadda ba zai iya taɓuka komai ba, sannan suka tafi da mashin ɗinsa.

KU KUMA KARANTA: Ranar zuma ta duniya: Amfani da sirrikan dake tattare da zuma

Sai dai rahotanni sun tabbatar da cewa ‘yan Arewa mazauna Legas sun yi iya ƙoƙarinsu wajen ganin an baiwa wannan ɗan Okada haƙƙinsa.

Yanzu haka shugaban hukumar ‘yan sanda na jihar Legas ya ziyarce shi a inda yake jinya, sannan an mayar masa da kuɗin belin da aka karɓa na mashin ɗinsa an kuma ba shi guduwmawa mai yawan gaske, kuma yana nan yanzu haka yana samun sauƙi sosai a unguwar Abbatuwa dake Legas.

Continue Reading

Hatsari

Fashewar bututun ɗanyen mai yayi sanadiyar mutuwar mutane 12

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Rivers ta tabbatar da cewa mutane 12 ne suka mutu sakamakon fashewar magudanar mai a safiyar Juma’a a yankin Rumuekpe da ke ƙaramar hukumar Emoha a jihar.

Kakakin ’yan sandan jihar, SP Grace Iringe-Koko, ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal, inda ta ce shaidar farko ya nuna waɗanda abin ya shafa na ɗiban ɗanyen man ne a lokacin da wurin ya kama wuta.

KU KUMA KARANTA: Kwastam ta kama tramadol ɗin naira miliyan 306 a Kaduna

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya tattaro cewa, hakan ya afku ne a yayin da wata motar bas ɗauke da ɗanyen mai ta kama wuta, yayin da take barin wurin zuwa wata matatar mai ta haramtacciyar hanya a yankin.

“Ya zuwa yanzu mutane 12 ana kyautata zaton sun ƙone kurmus. Har yanzu ba a gama sanin sunayen waɗanda abin ya shafa ba,” inji ta.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like