No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Najeriya a ƙarƙashin ministan ƙwadago, Mista Chris Ngige, sun maka ƙungiyar malaman jami’o’in Najeriya wato ASUU ƙara a kotun ɗa’ar ma’aikata.

A wata takardar da ministan ya tura kotun, Ngigen ya bayyana cewa suna so su sa halacci ko rashin halaccin tafiya yajin aikin a shari’ance.

In da za a iya tunawa, ƙungiyar ta ASUU tana yajin aiki ne tun kusan watanni 7 da suka shuɗe a bisa abin da ASUUn ta kira sakacin gwamnati da kuma rashin cika alƙɗawuran da gwamnatin ta ɗauka da kanta na inganta harkokin ilimin jami’a.

Wasu majiyoyi sun yi nuni da cewa ASUU ta shirya ɗaruruwan manyan lauyoyi masu darajar SAN domin tunkarar lamarin a kotu. Haka ita ma gwamnatin tarayyar ta shirya nata tawagar lauyoyin domin kalubalantar kungiyar.

Bayan zaman kotun da aka fara a yau a Abuja, kotun ta ɗage zaman zuwa ranar 16 ga wannan watan.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...