Amarya ta rasu ranar ɗaurin auren ta a Oyo

Wata amarya mai suna Rebecca Oyedotun ta faɗi ta mutu a ranar ɗaurin aurenta a garin Ogbomoso na jihar Oyo.

Mummunan lamarin ya faru ne a jajibirin ɗaurin auren marigayiyar a lokacin da ake shawagi da ƙawayenta.

A cewar mahaifin marigayiyar, Evangelist Oyedotun na Cocin C&S Reformed, da ke Isale-High School, amaryar ba ta nuna alamun rashin lafiya a baya ba har sai da ta faɗi da misalin ƙarfe 10:30 na safe.

Kafin ta rasu, amaryar za ta auri Abiodun Oluwadamilare a ranar Asabar, 19 ga watan Agusta, 2023.

A cewar ‘yar’uwar angon, shirye-shirye sun yi nisa kafin faruwar lamarin.

“Iyayen angon sun yanka saniyarsu a Ogbomoso, kuma kasancewarsa ɗansu tilo, angon, Abiodun, ya yi farin ciki, bai san cewa bala’i na nan zuwa ba.

KU KUMA KARANTA: Na fara alaƙa da wasu mata ne, saboda matata ta yi watsi da gidan auranta – wani Magidanci

Duk da cewa mahaifiyar marigayiyar, Misis Ruth Oyedotun, ba ta iya magana saboda baƙin ciki, mahaifin, Evangelist Oyedotun ya bayyana cewa sun kai amaryar nan take asibitin koyarwa na LAUTECH da fatan za ta dawo domin kammala bukukuwan aure.

“Mun kai ta asibitin koyarwa na LAUTECH da ke Ogbomoso. Bayan wani lokaci, ta farfaɗo, kuma ta bayyana a nutse, har zuwa wayewar garin Asabar, yanayinta ya tsananta don haka ta keɓe kan gado.

“An ma buƙaci mu kai ta Asibitin Koyarwa na Jami’ar Bowen don yin wasu gwaje-gwaje, wanda muka yi ba tare da ɓata lokaci ba.

“Ango ya suma yana kuka yana mai damuwa, ‘bari in tafi da ita.”

“Muna kwance a asibiti a tsawon wannan Asabar. Lafiyarta ta ƙara tsananta har sai da ta rasu a safiyar Lahadi, a cewar Tori News.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *