Connect with us

Rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti  bayan gajeruwar rashin lafiya.

Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.

Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.

Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Mahaifiyar tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff ta riga mu Gidan Gaskiya.

Mahaifiyar tsohon gwamnan, Hajja Aisa, ta koma ta Mahaliccinta ne a ranar Lahadi a Maiduguri, babban birnin jihar.

Ta rasu tana da shekaru 93, bayan fana da rashin lafiya.

Sanarwar rasuwar ta bayyana cewa za yi jana’izar Hajja Aisa da Azahar ranar Litinin 1 ga watan Yuli, 2024.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Za a yi jana’izar ne a gidant Marigayi Galadima Modu Sheriff d da ke Damboa Road a Maiduguri.
Sanarwar ta kuma roka wa marigayiyar gafara da kuma Aljannatul Firdaus.

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Wannan na cikin wani sako da tsohuwar jarumar masana’antar shirya fina-finan Hausa, Mansura Isah ta wallafa a shafinta na Instagram da safiyar ranar Talata.

Mansura ta wallafa cewar “Innalillahi wainna illahi raji’un, Allah Ya yi wa Fati Slow rasuwa.

“Allah Ya jikanta, Allah Ya yi mata rahama, ameen.”

KU KUMA KARANTA: Rasuwar Saratu Giɗaɗo ta girgiza masana’antar Kannywood

Mansura ta ce tsohuwar jarumar ta rasu ne a wani gari Abasha da ke kusa da Sudan, kuma tuni aka yi jana’izarta a can.

A cewarta yanzu haka ana zaman makokinta a gidansu da ke Unguwa Uku a Jihar Kano.

Fati Slow a baya ta fice a harkar fim din Hausa kafin daga bisani ta yi ɓatan-dabo.

Jarumar a shekarar da ta wuce ta sha tayar da ƙura a kafafen sada zumunta.

Tuni ‘yan masana’antar Kannywood da sauran al’ummar Musulmi suka shiga yi mata addu’ar samun rahama da Ubangiji.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like