No menu items!

Sample Page Title

Date:

Akwai yiyuwar nan gaba kaɗan Ganduje ya dawo jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Tsohon gwamnan Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Alhaji Sule Lamido, ya yi hasashen samun ɓaraka mai ƙarfi a cikin jam’iyyar APC mai mulki, inda ya ce nan ba da jimawa ba manyan jiga-jigan jam’iyyar ciki har da shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje na iya komawa jam’iyyar PDP.

Sule Lamido ya yi wannan ikirarin ne a yayin taron jam’iyyar PDP a ɗakin taro na Aminu Kano da ke Dutse a jihar Jigawa.

KU KUMA KARANTA:Najeriya ka iya zama kamar China idan aka koma tsarin jam’iyya daya – Ganduje

“Na tabbata waɗanda suka bar PDP za su dawo, domin APC cike take da rikici kuma nan bada dadewa ba gayyar zata watse” in ji Lamido.

Ya cigaba da cewa “Ku rubuta ku ajiye, nan da watanni shida, da yawa daga cikin waɗanda suka koma APC za su sake dawo PDP, kuma idan suka yi hakan, PDP za ta ƙara karfi mu karɓe mulki a shekarar 2027.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...