Duk me cewa Najeriya ba za ta gyaru ba, ba mutumin kirki ba ne – Ibrahim Khalil
Daga Jamilu Lawan Yakasai
Fitaccen malamin addinin musulunci da ke Kano, kuma Shugaban Majalisar malamai na Jihar kano, Malam Ibrahim Khalil ya ce
duk wanda ya tashi ya ganshi a Najeriya, tabbas Allah ne yayi masa zabi, saboda babu kamar ta a duniya.
KU KUMA KARANTA:Khuduba: An koma cin mutuncin addini da Malamai da Shugabanni ta hanyar amfani da sabuwar fasahar AI a duniya – Sheikh Sudais
Ya kuma ce duk wani abu da wata kasa ce alfahari da shi, tabbas akwai shi a Najeriya, don haka wajibi mutum ya mutunta kasar sa.
Kazalika yace cire tsammani daga gyarowar kasar, babban kuskure ne, domin matsalar kasar kawai rashin Shugaban ci ne.