Connect with us

Labarai

Akwai barazanar ambaliyar ruwa a jihar Kwara – NEMA

Published

on

Ofishin Hukumar Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da ke Minna ya sake sanar da wasu mazauna jihar Kwara kan wata ambaliyar ruwa da ke tafe.

Zainab Saidu, shugabar ofishin hukumar NEMA a Minna, ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa ana sa ran wannan ambaliya musamman a ƙananan hukumomin Ilorin ta Yamma da Ilorin ta Gabas na jihar.

Ta ce ana sa ran ƙananan hukumomin biyu za su fuskanci ambaliyar ruwa a cikin watannin Yuli da Nuwamba.

Misis Saidu ta ce hasashen yana ƙunshe ne a cikin hasashen ambaliyar ruwa na shekara-shekara da Hukumar Kula da Ruwa ta Najeriya, NIHSA, ta fitar a farkon shekarar.

“A cikin wannan hasashen, ƙananan hukumomin Ilorin ta Yamma da Ilorin ta Gabas an karkasa su ne a cikin yankunan da ake ƙira ‘Babban Hatsarin Ambaliyar Ruwa’ waɗanda ake hasashen za su fuskanci ambaliya daga watan Yuli zuwa ƙarshen shekara.

KU KUMA KARANTA: Uwargidan shugaban ƙasa ta bayar da tallafin kuɗi ga waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a Abuja

“Sauran ƙananan hukumomin kamar Patigi, Offa, Edu da Oyun, duk da ana ƙiransu da matsakaitan haɗarin ambaliya, suna iya fuskantar ambaliyar ruwa daga Yuli zuwa Nuwamba.

“Yana da kyau a lura cewa Kwara ta fara fuskantar ambaliyar ruwa da iska a wasu daga cikin waɗannan yankuna, don haka akwai buƙatar jama’a su yi taka-tsan-tsan don gujewa sake ɓarnatar dukiyoyi da asarar rayuka,” inji ta.

Madam Saidu ta buƙaci mazauna jihar a duk wuraren da aka gano su tabbatar da tsaftace magudanan ruwa domin gujewa toshewar hanyoyin ruwa.

“Waɗanda ke zaune a filayen ambaliya da bakin kogi dole ne a cikin gaggawa su shirya don ƙaura zuwa wurare mafi aminci da tsaro.

“Hakan ya faru ne saboda akwai alama mai ƙarfi da ke nuna cewa ruwan da ke gefen kogin Neja yana ƙaruwa kuma hakan zai ƙara ƙarfin magudanan ruwa.

“Saboda haka hakan zai haifar da ambaliya a bakin kogin kuma hakan zai yi tasiri sosai ga mazauna kewayen kogunan,” in ji ta.

Jami’in hukumar ta NEMA ya ƙara da cewa rigakafi ita ce hanya mafi inganci na maganin bala’o’i a duniya.

“Don haka dole ne jama’a su ɗauki nauyin bin waɗannan gargaɗin don ceton rayukansu da dukiyoyinsu.”

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Za a yi ruwan sama kamar da bakin ƙwarya a Abuja da maƙwabtanta – FEMA | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Gwamna Buni ya umurci ma’aikatar ayyuka da muhalli ta ƙara ƙarfafa matakan yaƙar ambaliyar ruwa a jihar | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: Gwamna Buni ya umurci ma’aikatar ayyuka da muhalli ta ƙara ƙarfafa matakan yaƙar ambaliyar ruwa a jihar - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like