No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ambaliyyar ruwa ta yi sanadiyyar mutuwar Mutane 50 a Jihar Neja

Daga Jameel Lawan Yakasai

Rahotanni daga Karamar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja, sun bayyana cewa ambaliyar ruwa mai tsananin karfi ta hallaka mutane da dama tare da lalata gidaje da kadarori na miliyoyin nairori.

Mazauna garin sun ce sakamakon ambaliyar ruwan, hanyar da ke hada shiyyar Arewa da Kudancin Najeriya ta karye.

To sai dai har zuwa yanzu ba a tabbatar da cikakken adadin wadanda suka mutu ba.

KU KUMA KARANTA: Yan Arewa su Shiryawa Ambaliyar Ruwa_ACF

Wasu daga cikin mazauna yankin sun bayyana cewa akalla mutane 50 ake zargin sun mutu wadanda yawancinsu mata ne da kananan yara, yayinda har zuwa Lokacin hada wannan rahoto ba akai da gano wasu daga cikin wadanda ruwa ya yi gaba da su ba.

Ambaliyar dai ta faru ne sakamakon ruwan sama mai karfi da aka yi a daren Laraba da ya dauki tsawon lokaci ya na zuba.

Rahotanni sun nuna cewe yadda alummar yankin ke rokon hukumomi da su kai musu daukin gaggawa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...