No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hisbah a Kano ta ja kunnen Amare da su daina zaman Majalisa idan mazajen su sun fita

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Hukumar da ke Umarni da kyakkyawan aiki, da hani da mummunan aiki ta Hisbah ta jihar Kano ta gargaɗi sabbin Amare su guji ɗabiʼar zaman majalisa da su ke yi da zarar mazajensu sun fita aiki musamman a sabbin unguwanni.

Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Dr. Mujahid Aminuddeen ne ya bayyana hakan ga Jaridar Neptune Prime a Kano

KU KUMA KARANTA:Ƙungiyar kiristoci a Kaduna ta nemi a bawa ‘ya’yanta aiki a hukumar Hisbah

Ya ce, zuwa yanzu Hisbah ta karbi korafe-korafe daga unguwanni mabanbanta kan wannan dabiʼar, kuma tuni suka shiga nazari don daukar matakin da ya dace.

Dr. Mujahid ya kuma yi kira ga magidanta da su sanya ido sannan su tsawatarwa matansu.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...