Hisbah a Kano ta rufe wasu shagunan da ake caca

0
47
Hisbah a Kano ta rufe wasu shagunan da ake caca

Hisbah a Kano ta rufe wasu shagunan da ake caca

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Hukumar dake hani da mummuna da umarni da kyakkyawa Hisbah tayi aikin data saba a cikin watan Ramadan.

Mataimakin Babban Kwamandan Hisbah na Jihar Kano Sheikh Mujahedeen Aminuddeen ne ya bayyana cewar hukumar ta rufe wasu shaguna da ake gudanar da caca a ciki cikin wata mai alfarma na Ramadan.

KU KUMA KARANTA:Hukumar Hisbah a Kano ta kama matasan da ba sa yin azumi da masu aikin banza

Hukumar tayi dirar mikiya a karamar hukumar minjibir dake Jihar Kano, inda suke kulle shagunan tare da kwashe kayan da ake gudanar da cacan duka dai karkashin jagorancin Kwamandan yankin.

Inda a karshe ya ja hankulan matasa da suji tsohon Allah, su mayar da hankulan su akan ibada.

Leave a Reply