Wata kotu ta tsare magidanci kan yi wa ’yarsa fyaɗe

0
42
Wata kotu ta tsare magidanci kan yi wa ’yarsa fyaɗe

Wata kotu ta tsare magidanci kan yi wa ’yarsa fyaɗe

Wata kotun Majistare da ke zamanta a Ado-Ekiti a hihar Ekiti, ta bayar da umarnin a tsare wani mutum mai shekara 42, Christopher Israel, a gidan gyaran hali bisa zargin yi wa ’yar cikinsa mai shekara 22 fyaɗe.

’Yansanda sun tuhumi Israel da laifin yin fyaɗe da kuma cin zarafi.

Alƙalin kotun, Misis Olubunmi Bamidele, ba ta amsa roƙon Israel na yin shari’ar a sirrance.

Ta bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake zargin a gidan gyaran hali da ke Ado Ekiti, har zuwa lokacin da za ta nemi shawarar lauyoyi daga ofishin daraktan ƙararrakin jama’a.

Ta ɗage shari’ar har zuwa ranar 6 ga watan Nuwamba, 2024.

KU KUMA KARANTA: Wata kotu a Kano ta bayar da belin ɗan jarida kan sukar gwamnatin jihar 

Tun da farko, mai gabatar da ƙara, Insifekta Olubu Apata, ya shaida wa kotun cewa Israel ya aikata laifin ne a ranar 21 ga watan Satumba a Ado-Ekiti.

Ya yi zargin cewa Israel ya yi wa ’yarsa mai shekara 22 fyaɗe, tare da ji mata rauni.

A cewarsa, laifin ya ci karo da tanadin sashe na 265 da na 256 na dokar laifuka ta Jihar Ekiti ta 2021.

Mai gabatar da ƙarar, ya buƙaci kotun da ta ci gaba da tsare Israel, har zuwa lokacin da ofishin DPP ya bayar da shawara kan shari’ar.

Leave a Reply