Connect with us

Labarai

Al’umma sun fita zanga-zanga kan tsadar rayuwa a jihar Neja

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

A yau Litinin da hantsi ne, ɗaruruwan al’umma a Minna da ke jihar Neja a Najeriya suka fito zanga-zanga kan tsadar rayuwa da ake fama da shi a ƙasar.

Masu zanga-zangar sun haɗa da mata da matasa inda suke rera waƙoƙii yayin da jami’an tsaro har da ‘yan sanda ke gefe suna kallo.

Wasu mazauna birnin da suka tattauna da BBC sun ce tsadar kayan masarufi da rashin taɓuka abin a zo a gani daga ɓangaren gwamnati wajen samar da sauƙi a lamarin ne ya tilasta musu rufe manyan tituna domin gwamnati ta ji kukansu.

KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga ta ɓarke a Senegal bayan sanar da ɗage zaɓe

Mataimakin gwamnan jihar Neja, Yakubu Garba a lokacin da yake yi wa masu zanga-zangar jawabi, ya ce gwamnati tana sane da irin ƙunci da wahalar da jama’a suke fuskanta a yanzu.

Ya ce gwamnati tana aiki domin rage halin matsi da aka shiga da kuma tasirin da ake gani sanadin cire tallafin mai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Za a fuskanci yunwa mai tsanani a arewa maso gabashin Najeriya – Majalisar Dinkin Duniya

Published

on

Za a fuskanci yunwa mai tsanani a arewa maso gabashin Najeriya – Majalisar Dinkin Duniya
https://collect-trump-cards.us/cgacor/
https://cttechnologynews.us/sgacor/
https://collect-trump-cards.us/vendor/
https://cutetimes.com/wp-admin/
https://carpetvacuumcleaner.com/jjs/
https://collect-trump-cards.us/generator/
https://cttechnologynews.us/product/
https://collect-trump-cards.us/thai/
https://cutetimes.com/dogol/
https://carpetvacuumcleaner.com/assets/
https://communio-vocation.com/
https://communio-vocation.com/jasa/
https://communio-vocation.com/vendor/
https://communio-vocation.com/admin/
https://antollino.com/js/
https://allthaicasino.com/filman/
https://allthaicasino.com/sgacor/
https://dreamsinsider.org/admin/
https://dreamlandgurkha.co.uk/wp-content/
http://dreammerch.net/wp-content/terbaru/
http://dreammerch.net/js/
https://adelrugs.com/film/
https://adelrugs.com/admin/
https://188.date/assets/
https://amjcorporation.co.uk/balajar/
https://amjcorporation.co.uk/sgacor/
https://blocktechy.com/sgacor/
https://blogsane.com/css/
https://bloomingpotcbd.com/xixi/
https://allthaicasino.com/
https://dreamsinsider.org/
https://dreamlandgurkha.co.uk/
http://dreammerch.net/
https://adelrugs.com/
https://188.date/
https://amjcorporation.co.uk/
https://blocktechy.com/sgacor/
https://blogsane.com/site/
https://bloomingpotcbd.com/vendor/
https://bloomingpotcbd.com/
https://blogsane.com/
https://blocktechy.com/

Za a fuskanci yunwa mai tsanani a arewa maso gabashin Najeriya – Majalisar Dinkin Duniya

Hukumar ayyukan jin ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce tana fafutukar tara isassun kuɗaɗe don magance matsalar ƙarancin abinci a yankin arewa maso gabashin Najeriya. Jami’ai sun ce ƙaruwar tashe tashen hankula a duniya sun sa ƙasashen da ke neman taimakon gwagwarmayar nema wa kansu mafita.

Koke-koken yara masu fama da larurar tamowa sun cika wani asibiti da ke arewa maso gabashin Najeriya, inda suke jira a yi musu jinyar ceton rai. Asibitin da ke garin Dikwa na da tazarar kilomita 90 daga tsakiyar babban birnin jihar.

An yi jinyar yara fiye da 300 a asibitin a wannan shekarar, kuma sabbin marasa lafiya na zuwa a duk rana. Mai’akatan jin ƙai sun ce ba su da isasshen wurin kula da dukkan marasa lafiyar.

Aliyu Muhammad Sani, shi ne jami’in kula da fannin masu larurar tamowa a asibitin, ya ce akwai majinyata sama da 45 da ke jira a kwantar da su asibitin, “abin da mu ke yi shi ne idan muka je zagayen duba marasa lafiya muka ga cewa akwai waɗanda suka murmure, da waɗanda suka warke, to sai mu sallamesu, a cewarsa.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya za ta kaɗa ƙuri’a kan tsagaita wuta a Gaza

Amma ga duk yaro ɗaya da aka sallama, jami’ai sun ce akwai kusan wasu 10 da ke jiran gurbinsa a asibitin. Kuma tsananin yanayin ciwo ne zai sa a tantace wanda ya cancanci a kwantar da shi.

Zainab Musa, wacce rikici ya raba da matsugunninta shekaru 10 da suka wuce, tana zama a Dikwa. Ta ce ana jinyar ɗaya daga cikin tagwayen ‘ya’yanta.

“Dana ya kamu da rashin lafiya saboda yunwa, ba na iya cin abinci yadda ya kamata don in shayar da su duka biyun. Amma a nan yanayinmu ya inganta, suna ciyar da ni sau uku a rana.”

Yayin da ake da ƙiyasin yara miliyan biyu da ke fama da larurar tamowa mai tsanani, asusun kula da yara na Majalisar Ɗinkin Duniya na UNICEF ya ce Najeriya ce ƙasa ta biyu a duniya da ta fi yawan yara da suka tsumbure.

Hukumar kula da ƙananan yara ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce a kowace sa’a, yara 100 ‘yan ƙasa da shekaru biyar a Najeriya ke mutuwa saboda rashin abinci mai gina jiki kuma kashi 20 cikin 100 na yara da ke fama da larurar ne kaɗai ke samun jinya.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki mataki ba, za a ga mummunan sakamako na ƙarancin abinci a wurare irin wannan.

Jami’ai sun ce matsalar ƙarancin abinci da matsalar rashin abinci mai gina jiki, su ne illolin tashe tashen hankulan ‘yan bindiga da aka daɗe ana yi a yankin, da sauyin yanayi da kuma manufofin gwamnati da suka sanya farashin kayan abinci ya yi tashin gwauron zabi.

Hauhawar farashin kayan abinci a Najeriya ya haura kashi 40 cikin 100, a cewar ofishin ƙididdiga na ƙasar.

A watan Mayu, Majalisar Ɗinkin Duniya da hukumomin Najeriya suka ƙaddamar da shirin neman gudummuwar dala miliyan 306 don magance matsalar ƙarancin abinci ga mutane kimanin miliyan 5 a jihohin da rikicin ya fi shafa.

Amma jami’ai sun ce gudummawar da ake bayarwa na raguwa.

“Idan aka yi la’akari da yanayin tallafin da Najeriya ke samu a cikin shekaru 10 da suka gabata, za a ga raguwar kuɗaɗen da ake samu sosai, saboda batun ba da fifiko ya shigo. Yawan rikice-rikice na ƙaruwa kusan a duk rana, ko wata-wata, ko shekara-shekara,” kamar yadda Mohamed Malik kodinetan Majalisar Ɗinkin Duniya a yankin ya bayyana.

Amma a Dikwa, ƙungiyoyin agaji na taimaka wa dubban mutane su yi noman abinci a gida ta amfani da hanyoyin da suka dace da yanayin.

“Waɗanda ke bin tsarin sun sami amfanin gona da yawa daga filayen da suka noma, sun nema wa kansu hanyoyin samun sauƙin rayuwa, ta yadda za su tabbatar da samun abinci,” a cewar Khalifa Muhammad, na ƙungiyar ‘Mercy Corps Agricultural and Livestock’.

A ranar Litinin 8 ga watan Yuli, Najeriya ta sanar da shirin cire haraji kan wasu kayayyakin abinci da suka haɗa da alkama da masara domin samun farashi mai sauƙi.

Amma in dai ba a ɗauki wani ƙwaƙƙwaran mataki ba, jami’ai sun ce makomar miliyoyin mutane, musamman yara na tattare da rashin tabbas.

Continue Reading

Labarai

Abin da ya sa ɗalibi ya fashe da kuka don ya faɗi a gasar ‘Spelling Bee’ a Yobe

Published

on

Abin da ya sa ɗalibi ya fashe da kuka don ya faɗi a gasar 'Spelling Bee' a Yobe

Abin da ya sa ɗalibi ya fashe da kuka don ya faɗi a gasar ‘Spelling Bee’ a Yobe

Ɗaya daga cikin ɗaliban da suka yi matuƙar ƙoƙari a gasar spelling Bee da aka gudanar a birnin Damaturun jihar Yobe, sai dai kash, a kusa da ƙarshe ya yi rashin nasara. Nan da nan yaro ya ke sharɓar kuka, ana ta lallaɓarsa amma ya ƙi ya yi shiru.

Daga baya an tambaye shi dalilin kukan, sai ya ce an masa alƙawarin idan har ya ci gasar za a saya masa keke.

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Yobe ya dakatar da shugaban ƙaramar hukumar Machina saboda halin rashin ɗa’a

To kuma ga shi bai ci gasar ba. Kenan ba za a saya masa wannan keke da ya ke shauƙi da buri ba.

A lokacin da Farfesa Ali Ibrahim Abbas ya ji wannan labari, shi ne ya ƙira yaron, aka je aka sayo masa sabon keke aka ba shi. Ta ke yaro ya hau murna da farin ciki.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Sakkwato ya karɓe ikon naɗa sarakuna da Hakimai daga hannun sarkin musulmi

Published

on

Gwamnan Sakkwato ya karɓe ikon naɗa sarakuna da Hakimai daga hannun sarkin musulmi

Gwamnan Sakkwato ya karɓe ikon naɗa sarakuna da Hakimai daga hannun sarkin musulmi

A ƙarshe dai gwamnan Sakkwato ya karɓe ikon naɗa sarakuna da suka haɗa da uwayen ƙasa da hakimai daga hannun mai alfarma Sarkin musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar III.

Wannan ya biyo bayan rattaɓa hannu da gwamnan ya yi ga dokar da Majalisar ƙananan hukumomi ta yi wa gyaran fuska.

Duk da yake an samu ƙorafe-ƙorafe da dama har daga manyan mutane akan ƙudurin gwamnatin Sakkwato na yin gyaran fuska ga dokar ƙananan hukumomi wadda daga cikin tanadin ta, akwai ikon naɗa uwayen ƙasa da hakimai, yanzu maganar ta zo ƙarshe, domin ƙudurin ya zama doka.

Sai dai saɓanin yadda mutane suka ɗauka a farko na ganin an rage wa sarkin musulmi ƙarfin iko, gwamna Ahamd Aliyu yace, ai an sha yin gyare-gyare ga dokoki a jihohi har ma da jihar Sakkwato.

Yace ba a yi wannan don cin zarafi ko ƙuntata wa wasu jama’a ba, sai dai don kawo ci gaba ga jama’ar Sakkwato.

Wannan dokar dai tana nufin yanzu Sarkin Musulmi ba shi da ikon naɗa sarakuna a ƙananan hukumomi, kamar yadda mataimakin mai tsawatarwa na Majalisar dokokin jihar sakkwato ɓangaren masu rinjaye Abubakar Shehu Yabo yace.

KU KUMA KARANTA:Ranar Lahadi ce 1 ga watan Muharram – Sarkin Musulmi

Wasu masu ruwa da tsaki a masarauta sun nuna rashin jin daɗin su a kan wannan dokar yayin da wasu suka ja hankalin gwamnati a kan ta nada Sarakuna wadanda suka mutu ba’a sake yin su ba.

Shi kuwa Malami Waziri ya bayyana ra’ayi ne cewa, yanzu dai a iya cewa takun saƙa a harkar masarauta a Sakkwato ta zo ƙarshe, domin an rufe wannan shafi, iko ya koma a hannun gwamna.

Yanzu hankali ya koma jihar Kano wadda yanzu haka ke da Sarakuna biyu, inda ake dakon ganin yadda za ta kaya, da ma jihohin Katsina da Kebbi, da su ma ke takun saka a kan sarauta.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like