Connect with us

Rasuwa

Yadda aka yi jana’izar Wazirin Borno, Mustapha Mukhtar

Published

on

A ranar Asabar aka yi jana’izar Wazirin Borno, Yerima Mustapha Muktar, wanda Imam Idaini na Borno, Shettima Mamman Saleh ya jagoranta a Maiduguri.

Shugaba Tinubu ya yi juyayinsa rasuwar Wazirin Borno, a sakon taziyyarsa ga Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ya kuma roƙi Allah ya ƙisan sa ya ba wa iyalansa juriyar rashin.

Yerima Mustapha  wanda ya zama Wazirin Borno a 2007, shi ne firaminista kuma babban mashawarcin Shehun Borno; ya rasu yana d shekaru 50, ya bar mahaifiyarsa da mata huɗu da yaya, 19 da kuma ’yan uwansa.

KU KUMA KARANTA: Wazirin Fika, Malam Adamu Fika, ya rasu yana da shekaru casa’in

Dubban jama’a sun halarci jana’izar Wazirin Borno, ciki har da Gwamnan Babagana Zulum da mataimakinsa Umar Usman Kadafur da Sanata Kaka Shehu Lawan da Ministan Noma Abubakar Kyari da sauran jami’an gwamnati.

Shehu Dikwa, Ibrahim Ibn Umar Ibrahim, da Shehun Bama, Umar Ibn Shehu Kyari, da Sarakin Damaturu Shehu Hashimi II El-Kanemi da kuma Sarkin Gazargamu, Tijjani Ibn Saleh Gaidam, na cikin mahalarta jana’izar.

Ga yadda jana’izar kasance:

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti  bayan gajeruwar rashin lafiya.

Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.

Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.

Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Mahaifiyar tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff ta riga mu Gidan Gaskiya.

Mahaifiyar tsohon gwamnan, Hajja Aisa, ta koma ta Mahaliccinta ne a ranar Lahadi a Maiduguri, babban birnin jihar.

Ta rasu tana da shekaru 93, bayan fana da rashin lafiya.

Sanarwar rasuwar ta bayyana cewa za yi jana’izar Hajja Aisa da Azahar ranar Litinin 1 ga watan Yuli, 2024.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Za a yi jana’izar ne a gidant Marigayi Galadima Modu Sheriff d da ke Damboa Road a Maiduguri.
Sanarwar ta kuma roka wa marigayiyar gafara da kuma Aljannatul Firdaus.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like