Connect with us

Ƙasashen Waje

Sama da rabin jama’ar Sudan na buƙatar agajin jinƙai – MƊD

Published

on

Kusan watanni bakwai bayan soma yaƙi tsakanin sojojin Sudan da kuma rundunar RSF, rikicin ya sa sama da rabin jama’ar ƙasar na buƙatar agajin jinƙai, wanda hakan ya sa ake fargabar za a iya sake shiga halin da aka shiga a lokacin yaƙin Darfur shekaru 20 da suka gabata.

“Abin da ke faruwa yana da nasaba da mummunar mugunta,” in ji jami’ar kula da ayyukan jinƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya a Afirka a ranar Juma’a.

Sudan ta shiga ruɗani tun bayan da aka soma yaƙi a tsakiyar Afrilun bana, a lokacin da aka soma takun saƙa wadda ta zama babban rikici tsakanin shugaban sojojin na Sudan Janar Abdel Fattah al- Burhan da kuma kwamandan rundunar Rapid Support Forces wato Janar Mohamed Hamdan Dagalo.

Sai dai Clementine Nkweta-Salami, wadda ita ce shugabar tsare-tsaren ayyukan jin kai ta Majalisar Ɗinkin Duniya a Sudan, ta shaida wa wani taron manema labarai na Majalisar Ɗinkin Duniya cewa “yanayin ya munana kuma yana da daga hankali” kuma “a gaskiya, muna da ƙarancin kalmomi da za mu bayyana munin abin da ke faruwa.” Ta jaddada cewa “Rikicin Sudan ya yi munin da irinsa kaɗan ne a duniya”.

KU KUMA KARANTA: MƊD ta koka kan yadda matsin rayuwa ke ƙara tsanani a Sudan

Ta ce ana ci gaba da gwabza faɗa duk da cewa ɓangarorin da ke gaba da juna sun rattaɓa hannu kan wata yarjejeniya bayan tattaunawar zaman lafiya a Jeddah da ke ƙasar Saudiyya, inda suka yi alƙawarin kare fararen hula tare da samar da agajin jin ƙai ba tare da tsangwama ba ga mutane miliyan 25 da ke buƙatar taimako.

Janarorin da ba sa ga maciji da juna sun amince su kama wata gidauniyar jin ƙai, tare da haɗin gwiwar Majalisar Ɗinkin Duniya, in ji Nkweta-Salami. Haka kuma bayan taron a ranar Litinin, Majalisar tana fatan janarorin su aiwatar da abubuwan da suka yi alƙawari a Jeddah.

Ta bayyana cewa ɓangaren lafiya na ƙasar – wanda sama da kaso 70 cikin 100 na ɓangaren na wuraren da ake rikici ba su aiki – inda majalisar ta nuna damuwarta sakamakon ɓarkewar cutar kwalara da maleriya da bakon dauro.

Abin da muka gani tana ƙaruwa ita ce yunwa,” in ji Nkweta-Salami, da kuma tsantsan rashin abinci ga yara.

Majalisar Ɗinkin Duniya na son tallafa wa kusan mutum miliyan 12 – wato kusan rabin waɗanda suke neman agaji. Sai dai buƙatar da majalisar ke da ita na kusan sama da dala biliyan 2.6 na agajin jinƙai a Sudan a 2023 kusan kaso ɗaya bisa uku ne kawai aka samu, inda Nkweta-Salami ta buƙaci aka ƙara samar da ƙarin kuɗi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Dakta Mas’ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Published

on

Dakta Mas'ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Dakta Mas’ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Daga Ibraheem El-Tafseer

Waye Dakta Mas’ud Pezeshkian sabon shugaban ƙasar Iran na 9 cikin shekaru 45 ataƙaice?

An haife shi a ranar 29 ga Satumba, 1954, a Mahabad, a yammacin lardin Azarbaijan, Dakta Mas’ud Pezeshkian ya wakilci birnin Tabriz da ke arewa maso yammacin kasar a majalisar dokokin Iran ta 12.

Ya riƙe muhimmin muƙamai a majalisar a Hukumomi daban-daban matakin gwamnatin tarayya, kuma ya zama ministan lafiya a lokacin mulkin Shugaba Mohammad Khatami (2001-2005). Duk da cewa an tsige shi bayan wasu lokuta saboda gaza cimma wasu ayyuka da kawo sauyi.

An zaɓe Pezeshkian a majalissar 8th, 9th, 10th, and 11th. A tsakanin shekarar 2016 zuwa 2020, ya kuma rike mukamin mataimakin shugaban majalisar na farko. A baya dai ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2013 da 2021 amma ya kasa samun nasara a lokuta biyun.

KU KUMA KARANTA: An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Dr. Mas’ud Pezeshkian likitan zuciya ne kuma me koyarwa, ya yi aiki a matsayin shugabar Jami’ar Tabriz ta Kimiyyar kiwon lafiya, kuma a halin yanzu memba ne na ma’aikatan ilimi a wannan babbar jami’a a arewacin Iran.

Bayan da ya samu amincewa daga babbar hukumar da ke sa ido kan zabukan kasar na ya tsaya takara a zaben na ranar 28 ga watan Yuni a watan da ya gabata. Ya gabatar da tsare-tsarensa, inda ya jaddada muhimmancin damka ayyuka ga kwararru kuma masu ilimi a gwamnatinsa.

Haka nan kuma ya bayyana Javad Zarif, tsohon ministan harkokin wajen kasar Iran a matsayin zabinsa na shugabancin ma’aikatar harkokin wajen kasar, yayin da ya sha alwashin aiwatar da umarnin Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

Pezeshkian a hukumance ya shiga takarar neman kujerar shugaban kasar a ranar 1 ga watan Yuni, rana ta uku ta rajista, a ma’aikatar harkokin cikin gida da ke Tehran, tare da rakiyar gungun magoya bayanta.

A muhawarar zagaye na biyu na zaben shugaban kasa, Pezeshkian ya bayyana mahimmancin kiyayewa da cika alkawura a matsayin wani muhimmin al’amari na kiyaye kyawawan halaye.

Ya jaddada muhimmancin nuna girmamawa ga daidaikun mutane, tabbatar da jin muryoyinsu, da bayar da shawarwari kan ayyuka bisa ka’idojin adalci da adalci.

Tsohon ministan lafiya ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da amana ke takawa wajen ciyar da al’umma gaba, tare da jaddada cewa gaskiya na da matukar muhimmanci wajen samar da amana a tsakanin al’umma.

Pezeshkian ya jaddada muhimmancin ba da fifiko kan dangantaka da kasashen dake makwabtaka da ita, da fadada huldar dake tsakanin kasashen duniya don bunkasa ci gaban kasar.

A lokuta da dama, ya nanata kudurinsa na mutunta tsarin dokokin Jamhuriyar Musulunci da kuma manufofin da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamene ya bayyana.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

Published

on

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra'ila

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ƙungiyar Hezbollah mai da ke Lebanon ta ƙaddamar da hare-haren rokoki fiye da 200 da jirage marasa matuƙa zuwa arewacin Isra’ila, a wani martani na kisan ɗaya daga cikin manyan kwamandojinta.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce an kashe sojanta da dama a hare-haren, na Hezbollah.

Sojojin na Isra’ila sun kuma ce sun mayar da martani kan mayaƙan ƙungiyar da sansanoninta da ke kudancin Lebanon.

Kafofin yaɗa labaran Lebanon sun ce mutum guda ya mutu a wani harin jirgi maras matuƙi da Isra’ila ta kai garin Houla.

Hare-haren na baya-bayan nan, sun kasance mafiya muni cikin watanni tara tsakanin kan iyakokin ƙasashen biyu.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

An kashe ɗaya daga cikin kwamandojin Hezbollaha wani hari ta sama da Isra’ila ta kai birnin Tyre na ƙasar Lebanon.

Mohammed Nimah Nasser, ya kasance ɗaya daga cikin manyan jagororin ƙungiyar, kafin kisan nasa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Wani jirgin ruwa ya kife da ‘yan ci-rani a tekun Mauritania

Published

on

Wani jirgin ruwa ya kife da 'yan ci-rani a tekun Mauritania

Wani jirgin ruwa ya kife da ‘yan ci-rani a tekun Mauritania

‘Yan ci-rani kimanin 90 ne suka rasu a kan hanyarsu ta zuwa Turai a lokacin da jirgin ruwan da suke ciki ya kife a farkon makon nan a gabar tekun Mauritania, in ji kafar watsa labarai ta ƙasar wadda ta ambato jami’ai na bayani a ranar Alhamis.

Ana kuma ci gaba da neman da dama da suka bata.

“Jami’an tsaron teku na Mauritania sun gano gawawwakin mutane 89 da suka hau wani babban jirgin ruwan masunta da ya kife a ranar Litinin 1 ga Yuli a gabar tekun Atlantika,” kusan nisan kilomita huɗu daga gabar garin Ndiago a kudu maso-yammacin kasar, in ji kamfanin dillancin labarai na Mauritania a ranar Alhamis.

Jami’an tsaron iyakokin tekun sun kuma kuɓutar da wasu mutanen tara, ciki har da wata yarinya ‘yar shekara biyar, in ji kafar yaɗa labaran.

Kamfanin dillancin labaran ya rawaito cewa wadanda suka kuɓuta na cewa jirgin nasu ya taso ne daga iyakar Senegal da Gambia dauke da fasinja 170, wanda hakan ya sanya ake neman mutane 72 da suka ɓata.

Wani babban jami’in karamar hukuma a yankin da ya nemi a boye sunansa ya tabbatar wa AFP aukuwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Hanyar tekun Atlantika na da hatsari sosai saboda manyan igiyar ruwa, kuma ‘yan ci-rani na yin lodin da ya haura ka’ida a jiragen ruwa, a mafi yawan lokuta jiragen ba su da ingancin shiga teku, kuma ba sa ɗaukar isassen ruwan sha.

Amma hakan ya sake fitowa fili ne sakamakon yadda ake ƙara sanya idanu kan tekun Bahar Rum.

A shekarar 2023 adadin ‘yan ci-rani da suke zuwa tsibiran Canary na Sifaniya ya ninka a shekara guda, wanda ya kai mutane 39,910, kamar yadda gwamnatin Sifaniya ta bayyana.

Tsibiran Canary na Sifaniya na daura da iyakar tekun arewacin Afirka da nisan kilomita 100.

Amma jiragen ruwa da dama – mafi yawansu na katako – na kama hanya daga Maroko, Yammacin Sahara, Mauritania, Gambia da Senegal don zuwa tsibiran na Sifaniya.

Sama da ‘yan ci-rani 5,000 ne suka mutu a teku yayin ƙoƙarin tsallaka wa Sifaniya a watanni biyar na farkon wannan shekarar, kenan mutane 33 ne ke mutuwa kowacce rana, kamar yadda Caminando Fronteras, wata ƙungiyar bayar da agaji ta Sifaniya ta bayyana.

Wannan ne adadin rasa rayuka mafi yawa tun bayan da kungiyar ta fara tattara bayanai a 2007, kuma mafi yawa na mutuwa ne a hanyar tekun Atlantika.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like