Za a gudanar da gasar tseren raƙuma mafi girma a Saudiyya

Hukumar da ke shirya gasar tseren raƙuma ta Saudiyya ta ce gasar tseren raƙuma da za a gudanar a wannan shakera a ƙasar za ta kasance mafi girma da aka taɓa yi a tarihin ƙasar.

Hukumar ta fitar da jadawalin gasar da ta ce za a kwashe kwanaki 38 ana gudanarwa.

Jadawalin gasar ya nuna cewa za a fara gasar wadda kusan mutum 600 za su fafata, cikin tsakiyar watan Agusta.

KU KUMA KARANTA: Rundunar Sojojin Najeriya na gudanar da gasar motsa jiki tsakanin sojojin ƙasar

Gasar wadda za a gudanar a birnin Taif ƙarƙashin jagorancin Yarima mai jiran gadon sarautar ƙasar Mohammed bin Salma, an shirya ta ne da nufin nuna muhimmanci da martabar raƙuma a al’adun ƙasar.

An tsara gudanar da gasar ne mataki-mataki, inda za a fara matakin farko na gasar a garin Tabuka, sannan a ƙarƙare gasar a birninTaif.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *