An binne gawar Oreoluwa Aina, ‘yar shekara 28 mai yiwa ƙasa hidima da hatsarin jirgin ƙasa da motar Bus ta BRT ta rutsa da ita a Legas, haɗarin da ya afku a ranar Alhamis, 9 ga watan Maris.
Oreoluwa na cikin mutane shida da aka tabbatar sun mutu bayan da jirgin ƙasa ya murƙushe wata motar bas ɗin ma’aikatan gwamnatin jihar Legas a yankin PWD da ke unguwar Ikeja a jihar.
KU KUMA KARANTA: Masu garkuwa sun kashe ɗan bautar ƙasa, bayan karɓar kuɗin fansa
An binne marigayiyar, wanda ke aikin bautar ƙasa a sashen kula da ayyukan karatu na ma’aikatar ilimi ta jihar Legas a Alausa a ranar asabar a makabartar Atan.
Tawagar gwamnatin jihar ƙarkashin jagorancin kwamishinan ilimi, Folasade Adefisayo ta halarci jana’izar.
Haka kuma akwai ‘yan uwan mamaciyar da kuma kodinetan hukumar NYSC ta jihar Legas, Yetunde Baderinwa.
Leave a Reply