Connect with us

Labarai

Kayan abinci na ya ƙare, wani Sanata ya koka

Published

on

Daga Haruna YUSUF, Abuja

Sanata Orji Uzor Kalu ya koka da yadda ake ci gaba da fama da ƙarancin takardun naira a Najeriya sakamakon matakan da babban bankin Najeriya (CBN) ya ɗauka na sake fasalin kuɗin ƙasar.

Sanata mai wakiltar mazaɓar Abia ta arewa a lokacin da yake mayar da martani game da matsalar kuɗi da ake fama a halin yanzu, ya ce iyalansa ba za su iya samun isassun kuɗin da za su yi girki ba.

Sanatan wanda tsohon gwamnan jihar Abia ne, ya bayyana haka ne a ranar litinin a lokacin da ya bayyana a wani shiri na gidan talabijin na Channels, wanda jaridar Neptune Prime ta bibiya.

“Kuna iya ganin manufar ya yi ƙaranci yayi daidai? Amma Ni ba na ajiye kuɗi a gidana, Ina shan wahala,” in ji shi.

KU KUMA KARANTA: CBN zai hukunta duk bankunan da ke ɓoye sabbin kuɗi

“A kwanakin baya, manajan gidana ya gaya wa matata da ke Abuja cewa ba mu da kuɗin da za mu dafa abinci.

“Matata kusan tana yawo kuma muna ciyar da mutane sama da 250 kowace rana. Wannan matsala ce a gare ni da kuma ga kowa da kowa.”

Jigon na jam’iyyar APC ya kasance na baya-bayan nan a cikin jiga-jigan jam’iyyar da suka fito fili suka yi magana kan ƙarancin naira tun bayan da babban bankin ya dage kan wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu.

Idan dai ba a manta ba kotun ƙoli ta bayar da umarnin cewa tsofaffin takardun kuɗi na N200, N500 da N1,000 na nan daram, biyo bayan umarnin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a makon da ya gabata a ranar Alhamis 16 ga watan Fabrairu a jawabinsa na ƙasa ya tsawaita amfani da tsohuwar takardar naira 200 kawai, har zuwa ranar 10 ga watan Afrilun 2023.

Sai dai kuma hakan bai yi wa wasu gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki daɗi ba, waɗanda ke da ra’ayin cewa sai an yi amfani da tsohuwar takardar naira a jihohinsu.

Da yake la’akari da lamarin, Sanata Kalu ya bayyana ra’ayi ɗaya da gwamnonin, inda ya ce da ya yi biyayya ga umarnin kotun ƙoli kan kuɗin naira idan shi ne shugaban ƙasa.

Ya ce, “Don haka ne idan na kasance a matsayin shugaban ƙasa kamar yadda na faɗa muku a baya, zan saurari hukuncin kotun koli.

“Kotun ƙoli a gare ni, ko suna da gaskiya ko ba daidai ba, ya kamata shugaban ƙasa ya bi doka kuma ya nemi babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF), Abubakar Malami, da ya sake duba kotun ƙoli.”

Sanata Orji Kalu ya ba da tabbacin cewa APC za ta yi nasara a zaɓukan duk da rashin samun kuɗin da ake da wasu gwamnonin ciki har da Sanatoci suka yi ikirarin hakan zai shafi kayan aiki a lokacin zaɓe.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like