Connect with us

Labarai

Na cika alkawuran da nayi wa ’yan Najeriya a lokacin yaƙin neman zaɓe – Buhari

Published

on

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa alkawuran da yayi a lokacin neman zaɓen 2015 wa ‘yan Najeriya gwamnatinsa ta cika. Shugaban ya bayyana haka ne a taron jami’ar tarayya karo na 7 da aka yi a garin Oye-Ekiti na jihar Ekiti, inda ya bayyana cewa ya bayar da gudunmawa a fannonin tattalin arziki, tsaro, da yaki da cin hanci da rashawa.

Ya ƙara da cewa shugaban ƙungiyar Benchers ta Najeriya Cif Wole Olanipekun (SAN) da tsohon manajan darakta na bankin First Bank Bisi Onasanya da kuma tsohon kyaftin din Super Eagles Segun Odegbami, an ba su lambar yabo saboda gudunmawar da suka bayar na ci gaban kasa.

Ya ce alkawuran da ya yi a lokacin yaƙin neman zaɓe sun ta’allaka ne kan inganta tattalin arziki, da inganta tsaro, da yaƙi da cin hanci da rashawa, ya kuma nuna jin daɗinsa da yadda waɗannan yankuna uku suka samu ci gaba sosai.

Da yake ƙarin haske, shugaba Buhari ya ce gwamnati mai ci ta ɗora Najeriya kan turɓar da ba za a iya dawowa da ita ba, duk da cewa kasar ba ta kai ga El Dorado ba.

Ya ce, “Bari in tunatar da kowa cewa tushen yaƙin neman zaɓena na zama shugaban ƙasa a 2015 shi ne alkawarin inganta tsaro, karfafa tattalin arziki, da yaki da cin hanci da rashawa.

Godiya mai yawa ga Allah Maɗaukakin Sarki, na yi karfin gwiwa wajen tabbatar da cewa mun cika alkawuran nan guda uku. “A lokacin da aka rantsar da ni, al’ummar kasar na fama da ta’addanci da sauran matsalolin rashin tsaro.

KU KUMA KARANTA:Saboda masu tara kuɗin haram muka sauya takardun kuɗi, inji Buhari

Ina mai tabbatar da cewa an yi yaƙi da ta’addanci kuma an yi nasara, domin an kwato duk yankunan da ƙungiyoyin ‘yan ta’adda su ka karɓa. Kuma a halin yanzu ta’addanci a Najeriya yana dab da zama tarihi.

“Har ila yau, abin lura shi ne, a karkashin jagorancina, Nijeriya ta tashi daga magudanar ruwa na kusan durkushewar tattalin arziki, ta zama kasa mafi karfin tattalin arziki a nahiyar. Wannan ba aiki bane mai sauki. Yana iya zama kawai sakamakon ingantaccen dabarun girma.

“Kafin a zaɓe ni a matsayin shugaban kasa a 2015, kasar ma ta fuskanci cin hanci da rashawa. Haka kuma ana jin cewa ayyukan da gwamnatina ta yi da suka hada da aiwatar da tsarin TSA, manufar bayar da bayanan sirri, da kuma kara kaimi wajen gurfanar da hukumomin yaki da cin hanci da rashawa, sun taimaka wajen dakile karuwar cin hanci da rashawa a kasar.

“Bugu da ƙari kan muhimman abubuwa guda uku, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta sake gyara fannin ilimi ta hanyar kara kudade don samar da jarin bil’adama da samar da ababen more rayuwa.

“Duk da cewa ba zai yuwu a ware dukkan kuɗaɗen da ƙasar nan ke da su a fannin ilimi ba, amma sanin kowa ne cewa gwamnatina tun daga ranar 29 ga watan Mayun 2015, ta ci gaba da kara yawan kudaden da ake ba fannin a kasafin kudinta na shekara.”

Shima da yake jawabi a wajen taron, mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Abayomi Fasina, ya bayyana cewa cibiyar ta zana wa kanta wani katafaren tsarin ilimi na kasa da kasa a cikin lokaci mai tsawo.

Fasina ta taya ɗaliban da suka yaye murnar samun nasarar karatunsu, sannan Fasina ta bukace su da su ci gaba da zama wakilai nagari a jami’ar da kuma kyautata sunanta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like