Connect with us

Labarai

Bai kamata a zargi APC ba, don ta gaji matsalar tsaro- Aminu Jaji

Published

on

Daraktan tuntuɓa da wayar da kai na ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Tinubu/Shettima na yankin arewa maso yamma, Aminu Jaji, ya ce jam’iyyar APC ta gaji rashin tsaro da ƙasar nan ke fama da ita, don haka ba zai yu a iya ɗora alhakin akan ta ba.

Jaji, tsohon shugaban kwamitin leken asiri da tsaro na cikin gida a majalisar wakilai, kuma tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Zamfara a shekarar 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar APC, ya bayyana hakan ne a yayin ganawa da manema labarai a Gusau, babban birnin jihar.

Tsohon ɗan majalisar ya ci gaba da cewa gwamnatin APC ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin an shawo kan matsalar tsaro.

KU KUMA KARANTA:APC ta ceto Najeriya daga wargajewa, Tunibu zai ɗora ya magance matsalar tsaro – Shinkafi

Jaji ya kuma ce yana da kwarin gwiwar cewa APC za ta yi nasara tare da rike kujerar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 mai zuwa, ya kuma kara da cewa yana da yaƙinin cewa jihar Zamfara ma za ta kai APC ga gaci.

“Ina da ƙwarin gwiwar cewa APC za ta ci gaba da riƙe kujerar ta a matakin ƙasa da jihar Zamfara, kuma idan aka zaɓi ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC a 2023, zai sa Najeriya da ‘yan Nijeriya su yi alfahari.

“Na tabbata Sanata Bola Ahmad Tinubu zai ɗauki batun rashin tsaro a matsayin abin mafi fifiko kuma zai magance shi yadda ya kamata.

“Mun san cewa gwamnatin APC ce ta gaji matsalolin tsaro kuma jam’iyyar ta yi duk abin da za ta iya wajen magance matsalar,” inji shi.

Jaji ya kuma ce rijiyar man da aka gano a jihar Gombe da Bauchi an samu nasara a lokacin mulkin Buhari ne, wanda a cewarsa wata babbar nasara ce da gwamnatin APC ta samu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like