No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga; Rabo Haladu.

WANI rikici ya barke a shalkwatar Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya da ke Abuja a ranar Alhamis.

Wasu matasa masu zanga-zanga sun hallara a ofishin jam’iyyar inda rahoton  ke nuna cewa masu zanga-zangar sun rika yin wakoki suna sukar shugaban jam’iyyar Abdullahi Adamu.

rahoton ya ce matasan sun fito daga Jihar Kogi ne, kuma sun isa shalkwatar ne yayin da jam’iyyar ke wani taro.

Masu zanga-zangar na nuna bacin ransu ne kan abin da suka kira “kwace tikitin takarar mukamin dan majalisar wakilai da aka yi wa wani gwaninsu” kuma aka mika shi ga wani mutumin na daban.

Jami’an tsaro sun kulle kofofin babban ofishin jam’iyyar yayin da suka ji masu zanga-zangar na ikirarin hana Abdullahi Adamu ficewa daga ginin.

admin
adminhttps://neptuneprimehausa.com
Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...