Connect with us

Labarai

Tinubu Ba zai musuluntar da Najeriya ba – Masari

Published

on

Gwamnan jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, ya bayyana ikirarin cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, zai musuluntar da Najeriya idan aka zaɓe shi shugaban kasa a 2023 a matsayin batu mara tushe.

Da yake magana a ranar talata a wani taron da ƙungiyar Kiristocin Arewa ‘yan siyasa a lokacin da suka tarɓi uwargidan Tinubu, Sanata Remi Tinubu, a kaduna, Masari ya ce ko makaho ne zai zaɓi Tinubu, domin ya fi ɗaukacin ‘yan takarar shugaban ƙasa.

Masari ya bayyana jihar Legas a matsayin ƙaramar Najeriya, inda ya ce Kiristoci da Musulmi da ma arna duk suna zaune a Legas amma duk da haka Tinubu yayi kokarin kawo cigaba a jihar.

“Ba wani tushe balle makama kan tsoron cewa Tinubu zai musuluntar da Najeriya, ba gaskiya bane, shin Buhari ya musulunta Najeriya bayan shekara bakwai yana mulki?

“Shin Obasanjo ya Kiristantar Najeriya bayan shekaru takwas yana mulki?

“Shin Jonathan ya mayar da Najeriya kasar Kirista bayan shekaru shida yana mulki? Inji shi.

A nasa jawabin, gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce babbar matsalar ƙasar nan, ita ce siyasa da baƙin ciki.

Ya bayyana cewa idan matasa maza da mata za su taru domin wani aiki na bai ɗaya ba tare da baƙin ciki ba, za a samu cigaba a ƙasa.

“Tarihi zai maimaita kansa,” a lokacin mulkin soja ƙarƙashin Janar Ibrahim Babangida ya koma mulkin farar hula, an yi zaɓe tsakanin MKO Abiola na SDP da Alhaji Bashir Tofa NRC, abokin takarar Abiola musulmi ne, tikitin takarar musulmi da musulmi ne ya lashe zaɓen, Tofa, wanda ya zaɓi abokin takararsa Kirista ya sha kaye a zaɓen. Don haka Tinubu ne zai ci zaɓe,” inji Ganduje

Shi ma da yake jawabi, gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-rufai, ya ce gwamnonin APC na arewa sun yanke shawarar marawa ɗan takarar shugaban ƙasa a kudancin ƙasar baya “domin haɗin kai, daidaito da adalci a ƙasar nan.

“Bayan mulkin shugaba Buhari, ya dace fadar shugaban ƙasa ta tafi kudu. Kuma mun yi taro a Katsina a gaban Gwamna Aminu Bello Masari inda ya ce a cikin dukkan masu neman takarar shugaban ƙasa mu mara wa Ahmed Tinubu saboda irin nasarorin da ya samu a lokacin da yake gwamnan Legas.”

KU KUMA KARANTA:Zan yi adalci ga kowa, alƙawarin Tinubu ga ‘yan Najeriya

Sanata Oluremi Tinubu, ta ce mijinta ba zai yiwa ‘yan Najeriya riƙon sakainar kashi ba idan har aka zaɓe shi a karagar mulki, inda ta bayyana shi a matsayin ma’aikacin aiki kuma mutum ne mai “cike da hankali”.

Shugaban ƙungiyar matasan Kiristocin arewa, Mista Isaac Abra, ya ce Tinubu ne ya fi kowa cancantar tsayawa takarar shugaban ƙasa saboda abubuwan da ya yi a baya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like