Connect with us

Labarai

Ƙungiyoyin dattawan arewa da na Ibo, sun koka kan yawan yawace-yawacen Tinubu

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ƙungiyar dattawan arewacin Najeriya da takwararta ta Ohanaeze Ndigbo mai kare muradun al’ummar Igbo da wasu ƙungiyoyin farar hula sun bayyana rashin jin daɗinsu game da tafiya zuwa Paris da shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi daidai lokacin da ƙasar ke fama da ƙaruwar matsalar tsaro.

A ranar Laraba 24 ga watan Janairu ne shugaba Tinubu ya tafi zuwa Faransa domin wata ziyara ta ƙashin kai.

Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Ajuri Ngelale ya fitar gabanin tafiyar, ta ce Tinubu zai koma Najeriya cikin makon farko na watan Fabarairu.

Sai dai ƙungiyoyin a hirarsu da jaridar Daily Trust sun koka cewa babu gaskiya cikin sanarwar tafiyar la’akari da yadda aka ƙira tafiyar ta “ƙashin kai”.

Matakin ƙungiyoyin na zuwa ne bayan da shi ma tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya soki Tinubu inda ya bayyana shakku game da maƙasudin tafiyar tasa zuwa Faransa yayin da ake fuskantar ƙaruwar matsalar ‘yan bindiga da sauran matsalolin tsaro da ke ci gaba da ta’azzara.

KU KUMA KARANTA: Ganganci ne Atiku ya ce Tinubu ba ya aikinsa yadda ya kamata – Fadar shugaban Najeriya

Sai dai Fadar shugaban ƙasar ta ce duk da cewa Tinubu ba ya ƙasar, yana aiki tuƙuru domin kawo sauƙin matsalolin kuma yana bai wa hukumomin tsaro dukkanin goyon bayan da suke buƙata domin samun nasara kan masu aikata miyagun laifuka da nufin fitar da Najeriya daga halin rashin tsaron da take ciki.

Tinubu dai ya sa ƙafa ya fice daga ƙasar yayin da ake tsokaci game da jerin hare-haren da aka kai a Filato da sace-sacen jama’a a Abuja, babban birnin ƙasar da kuma hari na baya-bayan nan na sace ɗalibai da malaman makaranta a jihar Ekiti da ke kudu maso yammacin Najeriya.

Ƙungiyar dattawan arewacin Najeriyar ta ce tafiyar ta Tinubu zuwa Paris a irin wannan yanayi da ake ciki a kasar manuniya ce cewa shugaban ya duƙufa ne wajen cimma ƙudurorinsa na kashin kai a maimakon bai wa yan Najeriya kwarin gwiwa a lokacin da suke bukatar hakan.

Daraktan yada labarai na ƙungiyar, Abdulazeez Sulaiman ya ce ƙungiyar tana ganin matakin na shugaban ƙasar na tabbatar da damuwar da ake nunawa cewa Najeriya ta faɗa cikin matsalar rashin shugabanci na gari da rashin nuna damuwa da tausayi.

A nata ɓangaren, ƙungiyar Ohanaeze Ndigbo ta yi allah-wadai da tafiyar ta shugaba Tinubu zuwa Paris a halin taɓarɓarewar tsaro da sauran ƙalubale da ake ciki.

Babban sakataren kungiyar, Mazi Okechukwu Isiguzoro ya ce bulaguron da Tinubu ya yi na zuwa ne a lokacin da ƙasar ke fuskantar ƙalubalen tattalin arziƙi.

Isiguzoro ya yi ƙira ga Tinubu da ya yi wa ‘yan Najeriya bayani dalilin yin irin waɗannan tafiye-tafiye.

Shi ma shugaban ƙungiyar tabbatar da jagoranci na gari, GGT, Mista Tunde Salman ya ce da alama shugaba Tinubu ya bai wa wasu manyan jami’ai har da mataimakin shugaban ƙasa damar tafiyar da al’amuran.

Ya ba da misali da wani ƙwarya-ƙwaryan taro da aka shirya kan tsaro game da ƙaruwar matsalar a arewacin Najeriya, inda mataimakin shugaban ƙasa da ministocin tsaro suka zama masu taka rawa sosai a taron.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like