No menu items!

Sample Page Title

Date:

Zaizayar ƙasa na barazana ga mazauna Unguwar Yamma dake Garko a Kano

Daga Jameel Lawan Yakasai

Alʼummar Unguwar Yamma da ke Karamar Hukumar Garko a Jihar Kano na neman ɗauki kan barazanar zaizayar kasa da suke fuskanta daga wani ƙaton rami da ke mamayar yankin.

Wannan na cikin wata sanarwa da Comr. Abbas Ibrahim Adam Kwanar Garko ya fitar a madadin masu kishin garin.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Neja ta hana yin bukukuwan babbar Sallah a jihar

Ya ce sun shafe tsawon lokaci suna fama da wannan matsalar da ke ci gaba da barazana ga rayuka da dukiyoyin mazauna yankin.

“Ga fargaba bisa la’akari da daminar bana, wacce tazo da karfin gaske, muddin mahukunta basu shawu kan wannan lamari ba, gaskiya rayuwarmu da ta iyayenmu da Mazauna wannan yanki na cikin barazana bisa rashin tabbas” a cewar sa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...