Tinubu zai gabatar da kasafin kuɗin baɗi na N27.5tr ranar laraba

0
175

Majalisar Zartarwa ta amince da naira tiriliyan 27.5 a matsayin kasafin kuɗin Najeriya na shekarar 2024.

Dangane da hakan ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gabatar wa Majalisar Tarayya kasafin a ranar Laraba mai zuwa.

Sakataren bincike da yaɗa labarai a Majalisar Tarayya, Dokta Ali Barde Umoru ya tabbatar da haka a yammacin yau.

A ƙunshin kasafin da Majalisar Zartarwar ta amince da shi, an tsaida farashin gangar mai a kan $73.96 da lissafin cewa za a rika hako ganguna miliyan 1.78 a rana da kuma farashin duk dala guda a kan N750.

Wannan ne cikakken kasafi na farko da Bola Tinubu zai gabatar wa majalisar tun bayan rantsar da shi a watan Mayun da ya wuce.

KU KUMA KARANTA: Babu ɗalibin da zai bar makaranta saboda rashin kuɗi a mulkina – Tinubu

Gabatar da kasafin ya nuna cewa Mista Tinubu zai ci gaba da tafiyar da tsarin kasafin kuɗin daga Janairu zuwa Disamba kamar yadda tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar.

Leave a Reply