No menu items!

Sample Page Title

Date:

Najeriya da Indiya za su yaƙi safarar miyagun ƙwayoyi

Daga Shafaatu Dauda Kano

Hukumar NDLEA ta Najeriya da hukumar NCB ta Indiya sun amince da ƙarfafa haɗin gwiwa domin yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi tsakanin ƙasashen biyu.

Shugabannin hukumomin biyu, Buba Marwa da Anurag Garg, sun bayyana hakan a wata ganawar da suka yi ta intanet, inda suka mayar da hankali kan hana shigowar ƙwayoyi kamar tramadol daga Indiya zuwa Najeriya.

KU KUMA KARANTA: Hukumar Kwastam da NAFDAC sun kama miyagun ƙwayoyi da kuɗinsu ya haura Miliyan 150

Marwa ya bayyana cewa irin waɗannan ƙwayoyi suna da illa ga lafiya da tsaro, kuma ya nemi taimakon Indiya wajen bawa jami’an NDLEA horo na musamman don samun nasarar shirin.

Wannan matakin ya biyo bayan yarjejeniyar fahimta da aka cimma tsakanin kasashen a shekarar 2023, a ƙoƙarin Najeriya na magance safarar ƙwayoyi.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...