Connect with us

Labarai

Na daina jin daɗin rayuwa, jiran lokacin mutuwa nake- Aminu Ɗantata

Published

on

Shahararren attajirin nan na jihar Kano kuma hamshakin ɗan kasuwa, Alhaji Aminu Ɗantata, ya bayyana cewa yanzu baya jin daɗin rayuwa, kuma yana fatan ya bar duniya cikin aminci da salama

Aminu Ɗantata mai shekaru 91 ya kuma nemi gafarar waɗanda yayi wa laifi kamar yadda ya ce shi na yafe wa waɗanda suka yi masa laifi idan akwai.

Ya bayyana haka ne a ranar talata, a lokacin da ya karɓi baƙuncin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Kashim Shettima, a gidansa da ke unguwar Ƙoki a ƙwaryar birnin Kano.

Ya ce shekarun baya ya zagaya faɗin Najeriya inda ya gana da mutane da kuma samun abokai a kusan dukkan jihohin tarayyar ƙasar nan amma da kyar ya iya kiran mutum 10 da ke raye cikin abokan nasa a yau.

“Na zagaya duk jihohin Najeriya kuma na yi abubuwa da mutane a duk faɗin jihohin, da yawa abokai na ne amma abin baƙin ciki, duk mutanen da na sani, da kyar na iya ƙiran guda 10 da ke raye.

KU KUMA KARANTA:Tinubu/Shettima: Wannan tikitin babbar nasara ce ga Jam’iyyar APC – Gwamna Buni

“Gaskiya, kamar yadda nake a yanzu, ina jiran lokaci na ne kawai, bana jin daɗin rayuwa a yanzu, Ina fatan na bar duniya da imani.

“Ina fata ban ɓata wa kowa rai ba a rayuwa, Idan na ɓata wa wani rai, ina fatan su gafarta mini. Idan wani ya yi mini laifi, na yafe ma shi.

“Yanzu ni kaɗai ne na rage a cikin iyalina da ke zaune da jikoki,” in ji shi.

Aminu Ɗantata, wanda kawu ne ga Aliko Ɗangote, hamshakin attajirin da ya fi kowa kuɗi a Afrika, ya yabawa Shettima kan ziyarar.

Shettima, wanda ya kai ziyarar a jihohin Jigawa da Kano, ya ce ziyarar na da nufin ganawa da dattawan jihohin biyu kan ayyukan ci gaba da ake yi a yankin arewa gabanin zaɓen 2023.

Ya kasance a jihar Jigawa ranar litinin, inda ya gana da sarakunan Hadeja, Adamu Abubakar-Maje; Sarkin Dutse, Nuhu Muhammad Sunusi; Sarkin Gumel, Ahmed Muhammad-Sani; Sarkin Kazaure, Najib Husseini-Adamu da Sarkin Ringim, Sayyadi Abubakar-Maumud.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like