No menu items!

Sample Page Title

Date:

Masu aikin ceto sun zaƙulo gawarwaki fiye da 20 daga tekun arewacin Senigal a ranar Laraba bayan da wani kwale-kwalen da ke ɗauke da baƙin haure da ke kan hanyar zuwa Turai ya nutse, kamar yadda wani gwamnan yankin ya shaida wa AFP.

Gwamnan yankin Saint-Louis Alioune Badara Samb ya fadi ta wayar tarho cewa, “An gano gawarwaki sama da 20,” ya kuma ƙara da cewa an kuma ceto wasu ƙarin mutane 20.

Badara Samb bai bayyana adadin fasinjojin da ke cikin jirgin ba amma waɗanda suka tsira sun shaidawa AFP cewa adadin ya kai ɗari.

KU KUMA KARANTA:An buƙaci ‘tsawaita wa’adin mulkin’ shugaban Senegal Macky Sall

Mamady Dianfo, wanda ya fito daga Casamance da ke kudancin ƙasar mai nisa, ya ce akwai fasinjoji kusan 300 a lokacin da kwale-kwalen ya tashi daga Senigal mako ɗaya da ya wuce.

Gaɓar tekun Senegal dai wani wuri ne da ake ƙara samun fitowar baƙin haure ‘yan Afirka da ke zuwa tsibirin Canary na Spain, tashar jiragen ruwa na shiga Turai.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...