No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

A wani faifayin bidiyo da ‘yan bindigar masu garkuwa da mutane suka fitar, sun nuna Amarya da sauran ‘yan bikin su 63 da suka yi garkuwa da su. ‘Yan bindigar sun bayyana cewa gwamnati ta daina ƙarya na rage adadin waɗanda suka kama, amarya da ‘yan biki 63 suka kama suke a hannun su yanzu haka, ba 35 kamar yadda gwamnati take ta sanarwa ba. Kuma har yanzu suna hannunsu.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun sace mahalarta ɗaurin aure 35 a Najeriya

A bidiyon shugaban masu garkuwa da mutanen ya bayyana cewa “waɗannan da kuke gani ni ne nake riƙe da su, idan ba a biya wannan kuɗi ba, Naira miliyan 100, to ba za mu sake su ba. Idan kuma akwai wanda zai iya ƙwace su, to ya zo ya gwada. Amarya kuma idan ba a zo an fansheta ba, za mu ɗaura mata aure da wani” inji shi

A cikin bidiyon an nuno Amarya da sauran ‘yan bikin su 63, suna roƙon gwamnati da ta taimaka ta karɓo su, suna faɗin “a taimaka a biya kuɗin fansar, a sake mu, mu dawo gida. Ba su cutar da mu ba ko kaɗan, tun da suka tafi da mu” inji su.

Kalli bidiyon a nan:

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...