No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Wakilinmu

Wasu ‘yan sanda a Abuja, babban birnin Najeriya sun kama tsohon Kwamishinan Ayyuka na jihar Kano, Mu’azu Magaji.

Lauyansa da kuma iyalansa sun tabbatar wa Wakilinmu cewa an kama tsohon Kwamishinan ne ranar Alhamis da daddare lokacin da yake kan hanyarsa ta komawa masaukinsa bayan ya gama harkokinsa na ranar.

Lauyansa, Barrister Garzali Datti Ahmad, ya shaida wa BBC Hausa cewa suna zargin gwamnatin Kano ce ta tura ‘yan sanda Abuja suka kama shi.

Mu’azu Magaji, wanda ake yi wa lakabi da Ɗan Sarauniya, ya dade yana sukar gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje tun ma kafin a sauke shi daga kan mukaminsa.

admin
adminhttps://neptuneprimehausa.com
Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...