No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kakakin majalisar wakilan Najeriya Femi Gbajabiamil, ya umarci mambobin ƙungiyar ASUU da su kwantar da hankulansu game da iƙirarin da malaman suka yi na cewa an biya su rabin albashin watan Oktoba.

A wata sanarwa da ya sanya wa hannu, kakakin majalisar wakilan ya ce suna aiki domin magance wannan matsala da ta sake tasowa.Ya ƙara da cewa shugaban ƙasa Muhammadu Buhari na son a duba wannan batu, domin magance shi.

“A lokacin da ASUU ta janye yajin aikinta mako uku da suka gabata, mun yi zaton cewa dalibai za su koma makarantu domin ci gaba da karatu a jami’o’in kasar”, in ji Gbajabiamila.

Ya ce Majalisa da ɓangaren zartarwa za su yi aiki tare domin magance matsalolin da suka haddasa yajin aikin, yana mai cewa yanzu haka majalisar na aiki a kan ƙudurin kasafin kuɗin 2023, wanda ya tanadar wa ƙungiyar kuɗaɗen da suke buƙata domin raya jami’o’in kasar.

3 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...