No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kotu tayi watsi da hukuncin zaɓen ƙananun hukumomin jihar Kano

Daga Shafaatu Dauda Kano

Kotun ɗaukaka kara dake Abuja, ta rushe hukuncin da babbar kotun tarayya dake jihar Kano ta yanke akan zaben kananan Hukumomin Kano.

Idan za’a iya tunawa jam’iyyar APC reshen jihar Kano da wasu mutane ne suka shigar da kara tare da neman a dakatar da zaɓen ƙananun hukumomin, daya gudana a shekarar data gabata saboda zargin cewa shugaban hukumar zabe ta jihar mamba ne a jam’iyyar NNPP mai mulkin Kano.

KU KUMA KARANTA:Kotu ta yanke hukuncin kisa ga matashin da ya kona masallata a Kano

Sai dai a yau Juma’a mai sharia Oyewumi, na kotun daukaka kara ya ce tun da farko babbar kotun tarayya bata da hurumin sauraron ƙarar ballantana ta yi hukunci akai.

Akan wannan hujja kotun ta amince da bukatar bangaren gwamnatin Kano, wajen yin watsi da hukuncin kotun baya

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...