No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kotu a Kano ta bada umarnin cigaba da tsare fitaccen dilalin Migayun Kwayoyi Suleiman Dan Wawu

Daga Jameel Lawan Yakasai

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta bayar da umarnin ci gaba da tsare wani fitaccen mai sayar da miyagunkwayoyi, Sulaiman Aminu, wanda aka fi sani da Danwawu.

Alkalin kotun, M.S. Shu’aibu, ya bayar da wannan umarni, bayan Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta gurfanar da wanda ake zargin.

KU KUMA KARANTA:‘Yan sanda sun kama dillalin ƙwaya a Kano, sun ƙwace tramadol ta naira milyan 25

Wata sanarwa da kakakin hukumar NDLEA ta jihar Kano Sadiq Maigatari ya fitar, ta ce an kama wanda ake zargin ne a wani samame da rundunar ‘yan sandan Kano ta kai gidansa, inda daga bisani aka mika shi ga hukumar ta NDLEA domin gudanar da cikakken bincike tare da gurfanar da shi gaban kotu

Mai Shari’a M.S. Shu’aibu ya ɗage sauraron karar zuwa ranar 16 ga watan Yuni mai zuwa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...