No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Tarayya ta sanar da ranakun hutun Babbar Sallah

Daga Jameel Lawan Yakasai

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Juma’a, 6 ga Yuni, da Litinin, 9 ga Yuni, 2025, a matsayin ranakun hutu domin bikin Sallah Babba na bana.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya sanar da hakan a madadin Gwamnatin Tarayya a cikin wata sanarwa da Babbar sakatariya ta ma’aikatar, Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Litinin.

KU KUMA KARANTA:Khuduba: An koma cin mutuncin addini da Malamai da Shugabanni ta hanyar amfani da sabuwar fasahar AI a duniya – Sheikh Sudais

Tunji-Ojo ya taya daukacin al’ummar Musulmi na cikin gida da na kasashen waje murnar wannan lokaci mai albarka.

Ya bukaci al’ummar Musulmi da su ci gaba da ɗaukar darasin sadaukarwa da gaskiya da Annabi Ibrahim (A.S) ya nuna, tare da amfani da wannan lokaci wajen yin addu’a domin zaman lafiya da ci gaban Najeriya.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...