No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Neja ta hana yin bukukuwan babbar Sallah a jihar

Daga Shafaatu Dauda Kano

Gwamnan Jihar Neja, Umaru Bago, ya bada umarnin rage shagulgulan bikin Sallah da dakatar da Hawan Bariki da sauran manyan tarukan Sallah a dukkan masarautun jihar.

Wannan umarni ya biyo bayan mummunar ambaliya da ta auku a Mokwa da kewaye, wacce ta yi sanadin salwantar rayuka da dukiyoyi.

KU KUMA KARANTA: Kifewar jirgin ruwa ta kashe mutane da dama a jihar Sokoto

Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Abubakar Usman, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba, inda ya ce an yanke wannan shawara a matsayin girmamawa ga wadanda lamarin ya rutsa da su, da kuma ba da damar yin addu’a ga waɗanda suka gamu da iftila’in.

Yayin da yake isar da umarnin Gwamnan ga masarautu, Sakataren Gwamnatin ya ce ambaliyar Mokwa na daya daga cikin abu mafi muni da aka taba fuskanta a jihar cikin shekaru masu yawa da suka shuɗe inda ta bar wasu ba gida, wasu kuma suka rasa ‘yan uwansu da dukiyoyinsu.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...