No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Aljeriya ta karrama limamin nan, Imam Walid Mehsas wanda kyanwa ta hau jinkinsa a daidai lokacin da yake jagorantar Sallar Taraweeh, inda cikin tausaya wa ya yi ta shafar kyanwar wadda ta sumbace shi kafin daga bisani ta sauka daga jikinsa don raɗin kanta.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan mata uku sun tsere a lokacin da ake ƙoƙarin safarar su zuwa ƙasar Libya

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta ne ya nuna yadda Imam Walid ya mu’amalanci kyanwar cikin kyawun yanayi, lamarin da ya ƙayatar da jama’a da dama hatta waɗanda ba Musulmai ba daga sassan duniya.

Limamin ya sha yabo da jinjina, yayin da manyan kafafen yaɗa labarai na duniya suka yi ta yaɗa wannan labarin.

Yanzu haka gwamnatin Aljeriya ta gayyace shi tare da shirya masa taron liyafa na musamman, inda Ministan Kula da Lamurran Addini na ƙasar, Dr. Youssaf Belmahdi ya yaba masa kan wannan kyakkyawar ɗabi’ar da ya nuna wa dabba.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...