No menu items!

Sample Page Title

Date:

Fitaccen ɗan kasuwa a Najeriya Alhaji Aminu Ɗantata ya rasu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Allah Ya yiwa fitaccen ɗan kasuwar Najeriya dake birnin Kano Alhaji Aminu Ɗantata rasuwa a daren ranar Juma’a.

Ya rasu ya na da shekaru 94 da haihuwa a duniya.

An haifi Marigayi Alhaji Aminu Ɗantata a ranar 19 Mayu na shekarar 1931 ya kuma koma ga Allah a ranar 28 ga watan Yuni na shekarar 2025.

KU KUMA KARANTA:Wakiliyar BBC Hausa Bilkisu Babangida ta rasu

Har zuwa yanzu ba a sanar da lokacin jana’izarsa ba a hukumance.

Ya koma ga Allah yana da ‘ya’ya 7 da jikoki da dama ,daga cikin ‘ya’yansa akwai Alhaji Tajuddeen Aminu Dantata sai kuma ɗan ‘yar uwarsa fitaccen attijirin Afrika Alhaji Aliko Ɗangote.

Allah Ya gafarta masa da rahama.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...