Connect with us

Kudanci

Daga hawansa gwamna Adeleke ya tsige sarakuna 3, ya kori ma’aikata 12,000

Published

on

Gwamnan jihar Osun, Sanata Ademola Adeleke ya kori ma’aikata 12,000 tare da bayar da umarnin tsige wasu sarakuna uku, ya kuma soke naɗin manyan sakatarorin dindindin guda 30 tare da daƙatar da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Osun (OSIEC)da kuma mambobin hukumar.

Tsohon gwamnan jihar Adegboyega Oyetola ne ya ɗauki korarrun ma’aikatan da sakatarorin dindindin 30 aiki a karshen watan Yuli.

Sarakunan da Adeleke ya tsige sun haɗa da Akinrun na Ikinrun Oba Yinusa Akadiri; Aree na Ire Oba Ademola Oluponle da Owa na Igbajo, Oba Gboyega Famodun.

Gwamnan ya umarci sarakunan su bar fadar, inda ya nemi jami’an tsaro su karbe karɓe ragamar fadar, Adeleke ya kuma soke naɗin manyan sakatarorin dindindin guda 30 tare da dakatar da shugaban OSIEC da kuma mambobin hukumar OSIEC.

Tsohon gwamna Adegboyega Oyetola ya ɗauki korarrun ma’aikatan da sakatarorin dindindin 30 aiki a karshen watan Yuli.

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan, Olawale Rasheed ya fitar, ya ce gwamnan ya sanya hannu kan umarnin zartarwa da suka shafi batutuwan sarauta, batutuwan naɗe-naɗe, kafa kwamitin bita, tantance ma’aikata da kuma batutuwan ɗaukar aiki.

“Dukkan ayyukan da gwamnatin jihar Osun ta yi a kowane matsayi a cikin ma’aikatu da hukumomi da kwamitoci bayan 17 ga Yuli, 2022 za a soke su.

“Dokar zartarwa ta biyar akan harkokin masarautu da naɗin sarakunan gargajiya, dukkanin naɗe-naɗen sarakunan gargajiya da gwamnatin jihar Osun ta yi bayan ranar 17 ga Yuli, 2022, an ba da umarnin sake duba su don tabbatar da bin ka’idojin da suka dace na ayyana sarauta da kuma dokokin kasa, al’ada da al’adun da suka shafi irin wadannan masarautun.

“Batun Ikirun, Iree da Igbajo, don gujewa tabɓarɓarewar doka da oda, an dage nadin na Akinrun na Ikinrun, Aree na Ire da Owa na Igbajo har sai an sake nazari.

” Bayan haka, fadar Akinrun na Ikirun, Aree na Iree da Owa na Igbajo su kasance babu kowa a ciki, yayin da aka umarci jami’an tsaro da su dauki nauyin ragamarsu”

Sakataren gwamnatin jihar Osun, Tesleem Igbalaye, a wata sanarwa da ya fitar ya kuma sanar da dakatar da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Osun Mista Segun Oladitan da mambobin hukumar, sauran sun haɗa da Yusuf Oyeniran, Suibat Adubi, Prince Yinka Ajiboye, Abosede Omibeku, Dosu Gidigbi, da Wahab Adewoyin.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Etsu Nupe ya naɗa sarakunan ƙauye 17, ya hore su akan zaman lafiya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hatsari

Jirgin sama mai sauƙar ungulu ya faɗo a Legas

Published

on

Wani jirgin sama mai sauƙar ungulu ya yi hatsari a yankin Ikeja da ke Jihar Legas a kudancin Najeriya.

Wani jami’in hukumar ba da agajin gaggawa ta Legas ya ce jirgin ya kama da wuta jim kaɗan bayan rikitowarsa da tsakar ranar Talata a kusa da filin jirgin sama na Murtala Muhammad.

KALLI CIKAKKEN BIDIYON ANAN:

Hukumar agajin gaggawa ta Najeriya, ‘National Emergency Management Agency’ (NEMA), ta ce mutum huɗu ne ke cikin jirgin kuma an ceto su da ransu.
Jami’in NEMA mai kula da sashen kudu maso yamma, Ibrahim Farinloye, ya ce ba su kai ga gano mamallakin jirgin ba ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Lamarin ya faru ne shekara uku bayan wani jirgin Helikwafta mallakar kamfanin Quorom Aviation ya faɗo a yankin Opebi na Legas ɗin a watan Agustan 2020.

Continue Reading

'Yansanda

Da wane dalili ‘yan sanda suka lakaɗa wa ɗan Okada duka a Legas?

Published

on

Wani ɗan Okada, mai suna Alasan Usman matashi mai ƙoƙarin neman na kansa domin rufawa kansa da ‘yan uwansa asiri.

A ranar jumu’a ‘yan sanda a jihar Legas suka tare shi suka ce ya kawo babur ɗinsa duk da dai bai san laifin da ya aikata ba, sai ya ƙi ya basu. Saboda ya ƙi basu suka masa duka sai kace ɓarawo sai da suka yi masa jina-jina yadda ba zai iya taɓuka komai ba, sannan suka tafi da mashin ɗinsa.

KU KUMA KARANTA: Ranar zuma ta duniya: Amfani da sirrikan dake tattare da zuma

Sai dai rahotanni sun tabbatar da cewa ‘yan Arewa mazauna Legas sun yi iya ƙoƙarinsu wajen ganin an baiwa wannan ɗan Okada haƙƙinsa.

Yanzu haka shugaban hukumar ‘yan sanda na jihar Legas ya ziyarce shi a inda yake jinya, sannan an mayar masa da kuɗin belin da aka karɓa na mashin ɗinsa an kuma ba shi guduwmawa mai yawan gaske, kuma yana nan yanzu haka yana samun sauƙi sosai a unguwar Abbatuwa dake Legas.

Continue Reading

Hatsari

Fashewar bututun ɗanyen mai yayi sanadiyar mutuwar mutane 12

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Rivers ta tabbatar da cewa mutane 12 ne suka mutu sakamakon fashewar magudanar mai a safiyar Juma’a a yankin Rumuekpe da ke ƙaramar hukumar Emoha a jihar.

Kakakin ’yan sandan jihar, SP Grace Iringe-Koko, ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal, inda ta ce shaidar farko ya nuna waɗanda abin ya shafa na ɗiban ɗanyen man ne a lokacin da wurin ya kama wuta.

KU KUMA KARANTA: Kwastam ta kama tramadol ɗin naira miliyan 306 a Kaduna

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya tattaro cewa, hakan ya afku ne a yayin da wata motar bas ɗauke da ɗanyen mai ta kama wuta, yayin da take barin wurin zuwa wata matatar mai ta haramtacciyar hanya a yankin.

“Ya zuwa yanzu mutane 12 ana kyautata zaton sun ƙone kurmus. Har yanzu ba a gama sanin sunayen waɗanda abin ya shafa ba,” inji ta.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like