No menu items!

Sample Page Title

Date:

Boko Haram a Yobe sun kashe mutane da dama da ƙona gidaje

Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun hallaka mutane da dama, suka ƙona gidaje da kantuna tare da wawushe kayayyaki a ƙauyen Mafa da ke ƙaramar hukumar Tarmuwa ta Jihar Yobe.

Mayaƙa sama da 50 ɗauke da muggan makamai a kan babura ne suka far wa ƙauyen a yammacin ranar Lahadi.

Jami’in hulɗa da Jama’a na ’Yan Sanda a Jihar Yobe, DSP Dungus Abdulkarim, ne ya tabbatar da harin a Damaturu a safiyar Litinin.

DSP Dungus ya ce shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) cewa “Zuwa yanzu ba mu tantance adadi rayukan da aka rasa ba, a harin da aka kai da misalin karfe 4 na ranar Lahadi.

“Wani daga ƙauyen Mafa ne ya kai rahoton harin ne a Babban Ofishin ’Yan Sanda na ƙaramar hukumar Tarmuwa.

KU KUMA KARANTA: Mun kashe ’yan boko haram 5, 44 sun miƙa wuya – Sojojin Najeriya

“Mayaƙan, ɗauke da manyan makamai har da RPG sun far wa gundumar Mafa, suka ƙona gidaje da kantuna.

“Sun kuma kashe mutane da dama, amma ba a kai ga tantance adadinsu ba,” in ji DSP Dungus.

Ya ƙara da cewa maharan sun kuma jefar da wasu takardu masu ɗauke da rubutun Larabci.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...