No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hedikwatar Jam’iyyar APC ta Ƙasa ta ce ba ta da masaniyar umarnin kotu da ke dakatar da shugaban jam’iyyar, Abdullahi Ganduje.

Mai ba jam’iyyar shawara ta fuskar shari’a, Farfesa Abdulkarim Kana, ya ce ba su sami umarnin Babbar Kotun Jihar Kano kan shugaban jam’iyyar, wanda shugabannin mazabarsa suka dakatar ba.

Ya bayyana wa manema labarai a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja ranar Laraba cewa, “mun ji dai ana magana kan umarnin kotun, amma dai bai zo hannunmu ba.

KU KUMA KARANTA: An kori Abdullahi Umar Ganduje daga jam’iyyar APC a mazaɓarsa

“Waɗanda suka dakatar da shi ba mambobin jam’iyyar APC ba ne, kuma ba sa cikin jagororinta ba ne a Jihar Kano. Ba mu san su ba,” in ji Farfesa Kana.

Ya ci gaba da cewa, “Shugabancin jam’iyyarmu ya riga ya rubuta wa shugaban ’yan sanda takardar korafi kan lamarin.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...