No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Jam’iyyar NNPP a jihar Kano ta ce kawo yanzu babu wanda ya tuntuɓeta game da shiga jam’iyyar APC.

Sanusi Bature Dawakin Tofa mai magana da yawun gwamna Abba Kabir Yusuf, ya shaidawa BBC cewa wannan ƙira ake cewa shugaban APC Ganduje ya yi musu a kwararo suka ji shi.

”Mun ji bayanin cewa ya miƙo wannan ƙoƙon bara na gwamna ya dawo jam’iyyar APC to amma abin mamaki shi ne, shi Ganduje a matsayinsa na tsohon gwamna da tsohon mataimakin gwamna ya fi kowa sanin hanyar da ake isarwa gwamna mai ci saƙo idan ana son ya je wurinsa”, in ji Sanusi.

Ya kuma ƙara cewa gwamna Abba Yusuf ba shi da wata matsaya ta barin jam’iyyarsa ko ƙin barin jam’iyyarsa.

”Amma maganar da muka ji ya faɗa, a kafafen yaɗa labarai na zumunta mu ka ji ta, kuma a nan mu ka barta’’

”Ka san ita siyasa ko in ce sauya sheƙa ta siyasa kamar canza gida ne, ba ka tashi lokaci ɗaya kawai ka ɗauki jakarka ka fita, ka ce wai ka canza gida.

KU KUMA KARANTA: Dalilanmu na shiga zawarcin ‘yan kwankwasiyya da jagoransu – Ganduje

“Akwai abubuwan da za ka iya yi kafin ka ce ka canja gida saboda don haka mu a wurinmu wannan saƙo mun ji ne kawai kamar a sama”, in ji shi.

Wannan yunƙuri na jam’iyyar APC na zuwa ne bayan umarni da shugaba Tinubu ya bayar, na cewa ɓangarorin biyu su je su sasanta da juna.

Wasu dai na ganin cewa abu ne mai matuƙar wuya waɗannan ɓangarori su iya ajiye rigingimun da ke tsakaninsu su yi aiki tare idan ta tabbata cewa za su haɗe, musamman kan wanda zai zama jagora.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...